< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
To the chief Musician, [A Psalm] of David, the servant of the LORD, who spake unto the LORD the words of this song in the day [that] the LORD delivered him from the hand of all his enemies, and from the hand of Saul: And he said, I will love thee, O LORD, my strength.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
The LORD [is] my rock, and my fortress, and my deliverer; my God, my strength, in whom I will trust; my buckler, and the horn of my salvation, [and] my high tower.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
I will call upon the LORD, [who is worthy] to be praised: so shall I be saved from mine enemies.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
The sorrows of death compassed me, and the floods of ungodly men made me afraid.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
The sorrows of hell compassed me about: the snares of death prevented me. (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
In my distress I called upon the LORD, and cried unto my God: he heard my voice out of his temple, and my cry came before him, [even] into his ears.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Then the earth shook and trembled; the foundations also of the hills moved and were shaken, because he was wroth.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
There went up a smoke out of his nostrils, and fire out of his mouth devoured: coals were kindled by it.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
He bowed the heavens also, and came down: and darkness [was] under his feet.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
And he rode upon a cherub, and did fly: yea, he did fly upon the wings of the wind.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
He made darkness his secret place; his pavilion round about him [were] dark waters [and] thick clouds of the skies.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
At the brightness [that was] before him his thick clouds passed, hail [stones] and coals of fire.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
The LORD also thundered in the heavens, and the Highest gave his voice; hail [stones] and coals of fire.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Yea, he sent out his arrows, and scattered them; and he shot out lightnings, and discomfited them.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Then the channels of waters were seen, and the foundations of the world were discovered at thy rebuke, O LORD, at the blast of the breath of thy nostrils.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
He sent from above, he took me, he drew me out of many waters.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
He delivered me from my strong enemy, and from them which hated me: for they were too strong for me.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
They prevented me in the day of my calamity: but the LORD was my stay.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
He brought me forth also into a large place; he delivered me, because he delighted in me.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
The LORD rewarded me according to my righteousness; according to the cleanness of my hands hath he recompensed me.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
For I have kept the ways of the LORD, and have not wickedly departed from my God.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
For all his judgments [were] before me, and I did not put away his statutes from me.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
I was also upright before him, and I kept myself from mine iniquity.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Therefore hath the LORD recompensed me according to my righteousness, according to the cleanness of my hands in his eyesight.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
With the merciful thou wilt shew thyself merciful; with an upright man thou wilt shew thyself upright;
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
With the pure thou wilt shew thyself pure; and with the froward thou wilt shew thyself froward.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
For thou wilt save the afflicted people; but wilt bring down high looks.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
For thou wilt light my candle: the LORD my God will enlighten my darkness.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
For by thee I have run through a troop; and by my God have I leaped over a wall.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
[As for] God, his way [is] perfect: the word of the LORD is tried: he [is] a buckler to all those that trust in him.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
For who [is] God save the LORD? or who [is] a rock save our God?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
[It is] God that girdeth me with strength, and maketh my way perfect.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
He maketh my feet like hinds’ [feet], and setteth me upon my high places.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
He teacheth my hands to war, so that a bow of steel is broken by mine arms.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Thou hast also given me the shield of thy salvation: and thy right hand hath holden me up, and thy gentleness hath made me great.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Thou hast enlarged my steps under me, that my feet did not slip.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
I have pursued mine enemies, and overtaken them: neither did I turn again till they were consumed.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
I have wounded them that they were not able to rise: they are fallen under my feet.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
For thou hast girded me with strength unto the battle: thou hast subdued under me those that rose up against me.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Thou hast also given me the necks of mine enemies; that I might destroy them that hate me.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
They cried, but [there was] none to save [them: even] unto the LORD, but he answered them not.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Then did I beat them small as the dust before the wind: I did cast them out as the dirt in the streets.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Thou hast delivered me from the strivings of the people; [and] thou hast made me the head of the heathen: a people [whom] I have not known shall serve me.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
As soon as they hear of me, they shall obey me: the strangers shall submit themselves unto me.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
The strangers shall fade away, and be afraid out of their close places.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
The LORD liveth; and blessed [be] my rock; and let the God of my salvation be exalted.
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
[It is] God that avengeth me, and subdueth the people under me.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
He delivereth me from mine enemies: yea, thou liftest me up above those that rise up against me: thou hast delivered me from the violent man.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Therefore will I give thanks unto thee, O LORD, among the heathen, and sing praises unto thy name.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Great deliverance giveth he to his king; and sheweth mercy to his anointed, to David, and to his seed for evermore.

< Zabura 18 >