< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Au chef des chantres. De David. Psaume. Éternel! Tu me sondes et tu me connais,
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Tu sais quand je m’assieds et quand je me lève, Tu pénètres de loin ma pensée;
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Tu sais quand je marche et quand je me couche, Et tu pénètres toutes mes voies.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Car la parole n’est pas sur ma langue, Que déjà, ô Éternel! Tu la connais entièrement.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Tu m’entoures par derrière et par devant, Et tu mets ta main sur moi.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Une science aussi merveilleuse est au-dessus de ma portée, Elle est trop élevée pour que je puisse la saisir.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Où irais-je loin de ton esprit, Et où fuirais-je loin de ta face?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
Si je monte aux cieux, tu y es; Si je me couche au séjour des morts, t’y voilà. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Si je prends les ailes de l’aurore, Et que j’aille habiter à l’extrémité de la mer,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Là aussi ta main me conduira, Et ta droite me saisira.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Si je dis: Au moins les ténèbres me couvriront, La nuit devient lumière autour de moi;
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Même les ténèbres ne sont pas obscures pour toi, La nuit brille comme le jour, Et les ténèbres comme la lumière.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
C’est toi qui as formé mes reins, Qui m’as tissé dans le sein de ma mère.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Je te loue de ce que je suis une créature si merveilleuse. Tes œuvres sont admirables, Et mon âme le reconnaît bien.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Mon corps n’était point caché devant toi, Lorsque j’ai été fait dans un lieu secret, Tissé dans les profondeurs de la terre.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Quand je n’étais qu’une masse informe, tes yeux me voyaient; Et sur ton livre étaient tous inscrits Les jours qui m’étaient destinés, Avant qu’aucun d’eux existât.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Que tes pensées, ô Dieu, me semblent impénétrables! Que le nombre en est grand!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Si je les compte, elles sont plus nombreuses que les grains de sable. Je m’éveille, et je suis encore avec toi.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
O Dieu, puisses-tu faire mourir le méchant! Hommes de sang, éloignez-vous de moi!
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Ils parlent de toi d’une manière criminelle, Ils prennent ton nom pour mentir, eux, tes ennemis!
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Éternel, n’aurais-je pas de la haine pour ceux qui te haïssent, Du dégoût pour ceux qui s’élèvent contre toi?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Je les hais d’une parfaite haine; Ils sont pour moi des ennemis.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Sonde-moi, ô Dieu, et connais mon cœur! Éprouve-moi, et connais mes pensées!
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
Regarde si je suis sur une mauvaise voie, Et conduis-moi sur la voie de l’éternité!

< Zabura 139 >