< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
J’aime l’Éternel, car il entend Ma voix, mes supplications;
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Car il a penché son oreille vers moi; Et je l’invoquerai toute ma vie.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Les liens de la mort m’avaient environné, Et les angoisses du sépulcre m’avaient saisi; J’étais en proie à la détresse et à la douleur. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Mais j’invoquai le nom de l’Éternel: O Éternel, sauve mon âme!
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
L’Éternel est miséricordieux et juste, Notre Dieu est plein de compassion;
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
L’Éternel garde les simples; J’étais malheureux, et il m’a sauvé.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Mon âme, retourne à ton repos, Car l’Éternel t’a fait du bien.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Oui, tu as délivré mon âme de la mort, Mes yeux des larmes, Mes pieds de la chute.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Je marcherai devant l’Éternel, Sur la terre des vivants.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
J’avais confiance, lorsque je disais: Je suis bien malheureux!
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Je disais dans mon angoisse: Tout homme est trompeur.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Comment rendrai-je à l’Éternel Tous ses bienfaits envers moi?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
J’élèverai la coupe des délivrances, Et j’invoquerai le nom de l’Éternel;
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
J’accomplirai mes vœux envers l’Éternel, En présence de tout son peuple.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Elle a du prix aux yeux de l’Éternel, La mort de ceux qui l’aiment.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Écoute-moi, ô Éternel! Car je suis ton serviteur, Ton serviteur, fils de ta servante. Tu as détaché mes liens.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Je t’offrirai un sacrifice d’actions de grâces, Et j’invoquerai le nom de l’Éternel;
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
J’accomplirai mes vœux envers l’Éternel, En présence de tout son peuple,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
Dans les parvis de la maison de l’Éternel, Au milieu de toi, Jérusalem! Louez l’Éternel!

< Zabura 116 >