< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Lord, thou hast proved me, and known me:
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Thou hast know my sitting down, and my rising up.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Thou hast understood my thoughts afar off: my path and my line thou hast searched out.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
And thou hast foreseen all my ways: for there is no speech in my tongue.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Behold, O Lord, thou hast known all things, the last and those of old: thou hast formed me, and hast laid thy hand upon me.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Thy knowledge is become wonderful to me: it is high, and I cannot reach to it.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Whither shall I go from thy spirit? or whither shall I flee from thy face?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
If I ascend into heaven, thou art there: if I descend into hell, thou art present. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
If I take my wings early in the morning, and dwell in the uttermost parts of the sea:
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Even there also shall thy hand lead me: and thy right hand shall hold me.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
And I said: Perhaps darkness shall cover me: and night shall be my light in my pleasures.
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
But darkness shall not be dark to thee, and night shall be light as day: the darkness thereof, and the light thereof are alike to thee.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
For thou hast possessed my reins: thou hast protected me from my mother’s womb.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
I will praise thee, for thou art fearfully magnified: wonderful are thy works, and my soul knoweth right well.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
My bone is not hidden from thee, which thou hast made in secret: and my substance in the lower parts of the earth.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Thy eyes did see my imperfect being, and in thy book all shall be written: days shall be formed, and no one in them.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
But to me thy friends, O God, are made exceedingly honourable: their principality is exceedingly strengthened.
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
I will number them, and they shall be multiplied above the sand: I rose up and am still with thee.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
If thou wilt kill the wicked, O God: ye men of blood, depart from me:
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Because you say in thought: They shall receive thy cities in vain.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Have I not hated them, O Lord, that hated thee: and pine away because of thy enemies?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
I have hated them with a perfect hatred: and they are become enemies to me.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Prove me, O God, and know my heart: examine me, and know my paths.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
And see if there be in me the way of iniquity: and lead me in the eternal way.

< Zabura 139 >