< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
I have loved, because the Lord will hear the voice of my prayer.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Because he hath inclined his ear unto me: and in my days I will call upon him.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
The sorrows of death have encompassed me: and the perils of hell have found me. I met with trouble and sorrow: (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
And I called upon the name of the Lord. O Lord, deliver my soul.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
The Lord is merciful and just, and our God sheweth mercy.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
The Lord is the keeper of little ones: I was little and he delivered me.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Turn, O my soul, into thy rest: for the Lord hath been bountiful to thee.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
For he hath delivered my soul from death: my eyes from tears, my feet from falling.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
I will please the Lord in the land of the living.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
I have believed, therefore have I spoken; but I have been humbled exceedingly.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
I said in my excess: Every man is a liar.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
What shall I render to the Lord, for all the things he hath rendered unto me?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
I will take the chalice of salvation; and I will call upon the name of the Lord.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
I will pay my vows to the Lord before all his people:
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Precious in the sight of the Lord is the death of his saints.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
O Lord, for I am thy servant: I am thy servant, and the son of thy handmaid. Thou hast broken my bonds:
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
I will sacrifice to thee the sacrifice of praise, and I will call upon the name of the Lord.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
I will pay my vows to the Lord in the sight of all his people:
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
In the courts of the house of the Lord, in the midst of thee, O Jerusalem.

< Zabura 116 >