< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
A Song. A Psalm by David. My heart is steadfast, God. I will sing and I will make music with my soul.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Wake up, harp and lyre! I will wake up the dawn.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
I will give thanks to you, Yahweh, among the nations. I will sing praises to you among the peoples.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
For your loving kindness is great above the heavens. Your faithfulness reaches to the skies.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Be exalted, God, above the heavens! Let your glory be over all the earth.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
That your beloved may be delivered, save with your right hand, and answer us.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God has spoken from his sanctuary: “In triumph, I will divide Shechem, and measure out the valley of Succoth.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Gilead is mine. Manasseh is mine. Ephraim also is my helmet. Judah is my scepter.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab is my wash pot. I will toss my sandal on Edom. I will shout over Philistia.”
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Who will bring me into the fortified city? Who will lead me to Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Haven’t you rejected us, God? You don’t go out, God, with our armies.
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give us help against the enemy, for the help of man is vain.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Through God, we will do valiantly, for it is he who will tread down our enemies.

< Zabura 108 >