< Zabura 107 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give thanks to Yahweh, for he is good, for his loving kindness endures forever.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let the redeemed by Yahweh say so, whom he has redeemed from the hand of the adversary,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
and gathered out of the lands, from the east and from the west, from the north and from the south.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
They wandered in the wilderness in a desert way. They found no city to live in.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Hungry and thirsty, their soul fainted in them.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Then they cried to Yahweh in their trouble, and he delivered them out of their distresses.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
He led them also by a straight way, that they might go to a city to live in.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them praise Yahweh for his loving kindness, for his wonderful deeds to the children of men!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
For he satisfies the longing soul. He fills the hungry soul with good.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Some sat in darkness and in the shadow of death, being bound in affliction and iron,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
because they rebelled against the words of God, and condemned the counsel of the Most High.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Therefore he brought down their heart with labor. They fell down, and there was no one to help.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried to Yahweh in their trouble, and he saved them out of their distresses.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
He brought them out of darkness and the shadow of death, and broke away their chains.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them praise Yahweh for his loving kindness, for his wonderful deeds to the children of men!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For he has broken the gates of bronze, and cut through bars of iron.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Fools are afflicted because of their disobedience, and because of their iniquities.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Their soul abhors all kinds of food. They draw near to the gates of death.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cry to Yahweh in their trouble, and he saves them out of their distresses.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sends his word, and heals them, and delivers them from their graves.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them praise Yahweh for his loving kindness, for his wonderful deeds to the children of men!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Let them offer the sacrifices of thanksgiving, and declare his deeds with singing.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Those who go down to the sea in ships, who do business in great waters,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
these see Yahweh’s deeds, and his wonders in the deep.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
For he commands, and raises the stormy wind, which lifts up its waves.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
They mount up to the sky; they go down again to the depths. Their soul melts away because of trouble.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They reel back and forth, and stagger like a drunken man, and are at their wits’ end.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Then they cry to Yahweh in their trouble, and he brings them out of their distress.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He makes the storm a calm, so that its waves are still.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Then they are glad because it is calm, so he brings them to their desired haven.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them praise Yahweh for his loving kindness, for his wonderful deeds for the children of men!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Let them exalt him also in the assembly of the people, and praise him in the seat of the elders.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He turns rivers into a desert, water springs into a thirsty ground,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
and a fruitful land into a salt waste, for the wickedness of those who dwell in it.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
He turns a desert into a pool of water, and a dry land into water springs.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
There he makes the hungry live, that they may prepare a city to live in,
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
sow fields, plant vineyards, and reap the fruits of increase.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
He blesses them also, so that they are multiplied greatly. He doesn’t allow their livestock to decrease.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Again, they are diminished and bowed down through oppression, trouble, and sorrow.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
He pours contempt on princes, and causes them to wander in a trackless waste.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Yet he lifts the needy out of their affliction, and increases their families like a flock.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
The upright will see it, and be glad. All the wicked will shut their mouths.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Whoever is wise will pay attention to these things. They will consider the loving kindnesses of Yahweh.

< Zabura 107 >