< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
By David. Praise Yahweh, my soul! All that is within me, praise his holy name!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Praise Yahweh, my soul, and don’t forget all his benefits,
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
who forgives all your sins, who heals all your diseases,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
who redeems your life from destruction, who crowns you with loving kindness and tender mercies,
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
who satisfies your desire with good things, so that your youth is renewed like the eagle’s.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Yahweh executes righteous acts, and justice for all who are oppressed.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
He made known his ways to Moses, his deeds to the children of Israel.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Yahweh is merciful and gracious, slow to anger, and abundant in loving kindness.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
He will not always accuse; neither will he stay angry forever.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
He has not dealt with us according to our sins, nor repaid us for our iniquities.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
For as the heavens are high above the earth, so great is his loving kindness toward those who fear him.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
As far as the east is from the west, so far has he removed our transgressions from us.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Like a father has compassion on his children, so Yahweh has compassion on those who fear him.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
For he knows how we are made. He remembers that we are dust.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
As for man, his days are like grass. As a flower of the field, so he flourishes.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
For the wind passes over it, and it is gone. Its place remembers it no more.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
But Yahweh’s loving kindness is from everlasting to everlasting with those who fear him, his righteousness to children’s children,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
to those who keep his covenant, to those who remember to obey his precepts.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Yahweh has established his throne in the heavens. His kingdom rules over all.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Praise Yahweh, you angels of his, who are mighty in strength, who fulfill his word, obeying the voice of his word.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Praise Yahweh, all you armies of his, you servants of his, who do his pleasure.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Praise Yahweh, all you works of his, in all places of his dominion. Praise Yahweh, my soul!

< Zabura 103 >