< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
A Prayer of the afflicted, when he is overwhelmed and pours out his complaint before Yahweh. Hear my prayer, Yahweh! Let my cry come to you.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Don’t hide your face from me in the day of my distress. Turn your ear to me. Answer me quickly in the day when I call.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
For my days consume away like smoke. My bones are burned as a torch.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
My heart is blighted like grass, and withered, for I forget to eat my bread.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
By reason of the voice of my groaning, my bones stick to my skin.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
I am like a pelican of the wilderness. I have become as an owl of the waste places.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
I watch, and have become like a sparrow that is alone on the housetop.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
My enemies reproach me all day. Those who are mad at me use my name as a curse.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
For I have eaten ashes like bread, and mixed my drink with tears,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
because of your indignation and your wrath; for you have taken me up and thrown me away.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
My days are like a long shadow. I have withered like grass.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
But you, Yahweh, will remain forever; your renown endures to all generations.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
You will arise and have mercy on Zion, for it is time to have pity on her. Yes, the set time has come.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
For your servants take pleasure in her stones, and have pity on her dust.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
So the nations will fear Yahweh’s name, all the kings of the earth your glory.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
For Yahweh has built up Zion. He has appeared in his glory.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
He has responded to the prayer of the destitute, and has not despised their prayer.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
This will be written for the generation to come. A people which will be created will praise Yah,
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
for he has looked down from the height of his sanctuary. From heaven, Yahweh saw the earth,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
to hear the groans of the prisoner, to free those who are condemned to death,
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
that men may declare Yahweh’s name in Zion, and his praise in Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
when the peoples are gathered together, the kingdoms, to serve Yahweh.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
He weakened my strength along the course. He shortened my days.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
I said, “My God, don’t take me away in the middle of my days. Your years are throughout all generations.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Of old, you laid the foundation of the earth. The heavens are the work of your hands.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
They will perish, but you will endure. Yes, all of them will wear out like a garment. You will change them like a cloak, and they will be changed.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
But you are the same. Your years will have no end.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
The children of your servants will continue. Their offspring will be established before you.”

< Zabura 102 >