< Karin Magana 31 >

1 Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
The words of King Lemuel—the revelation which his mother taught him:
2 “Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
“Oh, my son! Oh, son of my womb! Oh, son of my vows!
3 Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
Don’t give your strength to women, nor your ways to that which destroys kings.
4 “Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
It is not for kings, Lemuel, it is not for kings to drink wine, nor for princes to say, ‘Where is strong drink?’
5 don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
lest they drink, and forget the law, and pervert the justice due to anyone who is afflicted.
6 A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
Give strong drink to him who is ready to perish, and wine to the bitter in soul.
7 bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
Let him drink, and forget his poverty, and remember his misery no more.
8 “Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
Open your mouth for the mute, in the cause of all who are left desolate.
9 Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
Open your mouth, judge righteously, and serve justice to the poor and needy.”
10 Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
Who can find a worthy woman? For her value is far above rubies.
11 Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
The heart of her husband trusts in her. He shall have no lack of gain.
12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
She does him good, and not harm, all the days of her life.
13 Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
She seeks wool and flax, and works eagerly with her hands.
14 Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
She is like the merchant ships. She brings her bread from afar.
15 Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
She rises also while it is yet night, gives food to her household, and portions for her servant girls.
16 Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
She considers a field, and buys it. With the fruit of her hands, she plants a vineyard.
17 Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
She arms her waist with strength, and makes her arms strong.
18 Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
She perceives that her merchandise is profitable. Her lamp doesn’t go out by night.
19 Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
She lays her hands to the distaff, and her hands hold the spindle.
20 Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
She opens her arms to the poor; yes, she extends her hands to the needy.
21 Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
She is not afraid of the snow for her household, for all her household are clothed with scarlet.
22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
She makes for herself carpets of tapestry. Her clothing is fine linen and purple.
23 Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
Her husband is respected in the gates, when he sits among the elders of the land.
24 Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
She makes linen garments and sells them, and delivers sashes to the merchant.
25 Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
Strength and dignity are her clothing. She laughs at the time to come.
26 Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
She opens her mouth with wisdom. Kind instruction is on her tongue.
27 Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
She looks well to the ways of her household, and doesn’t eat the bread of idleness.
28 ’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
Her children rise up and call her blessed. Her husband also praises her:
29 “Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
“Many women do noble things, but you excel them all.”
30 Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
Charm is deceitful, and beauty is vain; but a woman who fears Yahweh, she shall be praised.
31 Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.
Give her of the fruit of her hands! Let her works praise her in the gates!

< Karin Magana 31 >