< Mai Hadishi 1 >

1 Kalmomin Malami, ɗan Dawuda, Sarki a Urushalima.
The words of the Preacher, the son of David, king in Jerusalem:
2 “Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami. “Gaba ɗaya ba amfani! Kome ba shi da amfani!”
“Vanity of vanities,” says the Preacher; “Vanity of vanities, all is vanity.”
3 Wace riba ce mutum yake samu daga wahalar da yake fama a duniya?
What does man gain from all his labor in which he labors under the sun?
4 Zamanai sukan zo zamanai su wuce, amma duniya tana nan har abada.
One generation goes, and another generation comes; but the earth remains forever.
5 Rana takan fito rana ta kuma fāɗi, ta kuma gaggauta zuwa inda takan fito.
The sun also rises, and the sun goes down, and hurries to its place where it rises.
6 Iska takan hura zuwa kudu ta kuma juya zuwa arewa; tă yi ta kewayewa, tă yi ta koma inda take fitowa.
The wind goes toward the south, and turns around to the north. It turns around continually as it goes, and the wind returns again to its courses.
7 Dukan rafuffuka sukan gangara zuwa teku, duk da haka teku ba ya cika. Daga inda rafuffukan suke fitowa, a can suke komawa kuma.
All the rivers run into the sea, yet the sea is not full. To the place where the rivers flow, there they flow again.
8 Dukan abubuwa suna kawo gajiya, gaban magana. Ido ba ya gaji da gani, haka ma kunne yă ƙoshi da ji.
All things are full of weariness beyond uttering. The eye is not satisfied with seeing, nor the ear filled with hearing.
9 Abin da ya taɓa kasancewa, zai sāke kasance, abin da aka yi za a sāke yi kuma; babu wani abu sabo a duniya.
That which has been is that which shall be, and that which has been done is that which shall be done; and there is no new thing under the sun.
10 Akwai wani abin da za a ce, “Duba! Ga wani abu sabo”? Abin yana nan, tun dā can, ya kasance kafin lokacinmu.
Is there a thing of which it may be said, “Behold, this is new”? It has been long ago, in the ages which were before us.
11 Ba a tunawa da mutanen dā, haka su ma da ba a haifa ba tukuna waɗanda za su biyo bayansu ba za a tuna da su ba.
There is no memory of the former; neither shall there be any memory of the latter that are to come, among those that shall come after.
12 Ni, Malami, sarki ne bisa Isra’ila a Urushalima.
I, the Preacher, was king over Israel in Jerusalem.
13 Na dauri aniyata in gwada don in bincika ta wurin hikima dukan abin da ake yi a duniya. Kaya mai nauyi ne Allah ya ɗora a kan mutane!
I applied my heart to seek and to search out by wisdom concerning all that is done under the sky. It is a heavy burden that God has given to the sons of men to be afflicted with.
14 Na ga dukan abubuwan da ake yi a duniya, dukansu ba su da amfani, naushin iska ne kawai.
I have seen all the works that are done under the sun; and behold, all is vanity and a chasing after wind.
15 Abin da yake tanƙwararre ba zai miƙu ba; ba za a kuma iya ƙidaya abin da ba shi ba.
That which is crooked can’t be made straight; and that which is lacking can’t be counted.
16 Na yi tunani a raina na ce, “Duba, na yi girma, na kuma ƙaru da hikima fiye da duk wanda ya taɓa mulki a bisa Urushalima kafin ni; na ɗanɗana hikima mai yawa da kuma ilimi.”
I said to myself, “Behold, I have obtained for myself great wisdom above all who were before me in Jerusalem. Yes, my heart has had great experience of wisdom and knowledge.”
17 Sa’an nan na ɗaura aniyata ga fahimtar hikima, in kuma san bambanci tsakanin hauka da wauta, amma na koyi cewa wannan ma, naushin iska ne kawai.
I applied my heart to know wisdom, and to know madness and folly. I perceived that this also was a chasing after wind.
18 Gama yawan hikima yakan kawo yawan baƙin ciki; yawan sani, yawan ɓacin rai.
For in much wisdom is much grief; and he who increases knowledge increases sorrow.

< Mai Hadishi 1 >