< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Don’t be envious of evil men, neither desire to be with them;
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
for their hearts plot violence and their lips talk about mischief.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Through wisdom a house is built; by understanding it is established;
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
by knowledge the rooms are filled with all rare and beautiful treasure.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
A wise man has great power. A knowledgeable man increases strength,
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
for by wise guidance you wage your war, and victory is in many advisors.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Wisdom is too high for a fool. He doesn’t open his mouth in the gate.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
One who plots to do evil will be called a schemer.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
The schemes of folly are sin. The mocker is detested by men.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
If you falter in the time of trouble, your strength is small.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Rescue those who are being led away to death! Indeed, hold back those who are staggering to the slaughter!
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
If you say, “Behold, we didn’t know this,” doesn’t he who weighs the hearts consider it? He who keeps your soul, doesn’t he know it? Shall he not render to every man according to his work?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
My son, eat honey, for it is good, the droppings of the honeycomb, which are sweet to your taste;
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
so you shall know wisdom to be to your soul. If you have found it, then there will be a reward: Your hope will not be cut off.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Don’t lay in wait, wicked man, against the habitation of the righteous. Don’t destroy his resting place;
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
for a righteous man falls seven times and rises up again, but the wicked are overthrown by calamity.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Don’t rejoice when your enemy falls. Don’t let your heart be glad when he is overthrown,
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
lest Yahweh see it, and it displease him, and he turn away his wrath from him.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Don’t fret yourself because of evildoers, neither be envious of the wicked;
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
for there will be no reward to the evil man. The lamp of the wicked will be snuffed out.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
My son, fear Yahweh and the king. Don’t join those who are rebellious,
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
for their calamity will rise suddenly. Who knows what destruction may come from them both?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
These also are sayings of the wise: To show partiality in judgment is not good.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
He who says to the wicked, “You are righteous,” peoples will curse him, and nations will abhor him—
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
but it will go well with those who convict the guilty, and a rich blessing will come on them.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
An honest answer is like a kiss on the lips.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prepare your work outside, and get your fields ready. Afterwards, build your house.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Don’t be a witness against your neighbor without cause. Don’t deceive with your lips.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Don’t say, “I will do to him as he has done to me; I will repay the man according to his work.”
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
I went by the field of the sluggard, by the vineyard of the man void of understanding.
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
Behold, it was all grown over with thorns. Its surface was covered with nettles, and its stone wall was broken down.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Then I saw, and considered well. I saw, and received instruction:
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
a little sleep, a little slumber, a little folding of the hands to sleep,
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
so your poverty will come as a robber and your want as an armed man.

< Karin Magana 24 >