< Luka 17 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
He said to the disciples, “It is impossible that no occasions of stumbling should come, but woe to him through whom they come!
2 Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
It would be better for him if a millstone were hung around his neck, and he were thrown into the sea, rather than that he should cause one of these little ones to stumble.
3 Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
Be careful. If your brother sins against you, rebuke him. If he repents, forgive him.
4 In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
If he sins against you seven times in the day, and seven times returns, saying, ‘I repent,’ you shall forgive him.”
5 Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
The emissaries said to the Lord, “Increase our faith.”
6 Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
The Lord said, “If you had faith like a grain of mustard seed, you would tell this sycamore tree, ‘Be uprooted and be planted in the sea,’ and it would obey you.
7 “In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
But who is there amongst you, having a servant ploughing or keeping sheep, that will say when he comes in from the field, ‘Come immediately and sit down at the table’?
8 Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
Wouldn’t he rather tell him, ‘Prepare my supper, clothe yourself properly, and serve me while I eat and drink. Afterward you shall eat and drink’?
9 Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
Does he thank that servant because he did the things that were commanded? I think not.
10 Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
Even so you also, when you have done all the things that are commanded you, say, ‘We are unworthy servants. We have done our duty.’”
11 Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
As he was on his way to Jerusalem, he was passing along the borders of Samaria and Galilee.
12 Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
As he entered into a certain village, ten men who were lepers met him, who stood at a distance.
13 suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
They lifted up their voices, saying, “Yeshua, Master, have mercy on us!”
14 Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
When he saw them, he said to them, “Go and show yourselves to the priests.” As they went, they were cleansed.
15 Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
One of them, when he saw that he was healed, turned back, glorifying God with a loud voice.
16 Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
He fell on his face at Yeshua’s feet, giving him thanks; and he was a Samaritan.
17 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
Yeshua answered, “Weren’t the ten cleansed? But where are the nine?
18 Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
Were there none found who returned to give glory to God, except this foreigner?”
19 Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Then he said to him, “Get up, and go your way. Your faith has healed you.”
20 Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
Being asked by the Pharisees when God’s Kingdom would come, he answered them, “God’s Kingdom doesn’t come with observation;
21 Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
neither will they say, ‘Look, here!’ or, ‘Look, there!’ for behold, God’s Kingdom is within you.”
22 Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
He said to the disciples, “The days will come when you will desire to see one of the days of the Son of Man, and you will not see it.
23 Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
They will tell you, ‘Look, here!’ or ‘Look, there!’ Don’t go away or follow after them,
24 Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
for as the lightning, when it flashes out of one part under the sky, shines to another part under the sky, so will the Son of Man be in his day.
25 Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
But first, he must suffer many things and be rejected by this generation.
26 “Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
As it was in the days of Noah, even so it will also be in the days of the Son of Man.
27 Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
They ate, they drank, they married, and they were given in marriage until the day that Noah entered into the ship, and the flood came and destroyed them all.
28 “Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
Likewise, even as it was in the days of Lot: they ate, they drank, they bought, they sold, they planted, they built;
29 Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
but in the day that Lot went out from Sodom, it rained fire and sulphur from the sky and destroyed them all.
30 “Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
It will be the same way in the day that the Son of Man is revealed.
31 A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
In that day, he who will be on the housetop and his goods in the house, let him not go down to take them away. Let him who is in the field likewise not turn back.
32 Ku tuna fa da matar Lot!
Remember Lot’s wife!
33 Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
Whoever seeks to save his life loses it, but whoever loses his life preserves it.
34 Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
I tell you, in that night there will be two people in one bed. One will be taken and the other will be left.
35 Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
There will be two grinding grain together. One will be taken and the other will be left.”
37 Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”
They, answering, asked him, “Where, Lord?” He said to them, “Where the body is, there the vultures will also be gathered together.”

< Luka 17 >