< Yoshuwa 5 >

1 To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
As soon as all the kings of the Amorites on the west side of the Jordan, and all the kings of the Canaanites, who were along the coast of the Great Sea, heard that Yahweh had dried up the waters of the Jordan until the people of Israel had crossed over, their hearts melted, and there was no longer any spirit in them because of the people of Israel.
2 A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
At that time Yahweh said to Joshua, “Make flint knives and once more circumcise all the males of Israel.”
3 Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
Then Joshua made himself flint knives and he circumcised all the males of Israel at Gibeath Haaraloth.
4 Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
This is the reason Joshua circumcised them: All the males who had come out of Egypt, including all the men of war, had died in the wilderness along the way, after they came out from Egypt.
5 Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
Though all the males who came out of Egypt were circumcised, still, none of the boys born in the wilderness on the way out of Egypt had been circumcised.
6 Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
For the people of Israel walked forty years in the wilderness until all the people, that is, all the men of war who had come out of Egypt, died, because they did not obey the voice of Yahweh. Yahweh swore to them that he would not let them see the land that he had sworn to their ancestors that he would give to us, a land flowing with milk and honey.
7 Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
It was their children that Yahweh raised up in their place that Joshua circumcised, because they had not been circumcised on the way.
8 Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
When they were all circumcised, they remained where they were in the camp until they healed.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
Then Yahweh said to Joshua, “This day I have rolled away the disgrace of Egypt from you.” So, the name of that place has been called Gilgal until this present day.
10 Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
The people of Israel camped at Gilgal. They kept the Passover on the fourteenth day of the month, in the evening, on the plains of Jericho.
11 A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
On the day after Passover, that same day, they ate some of the produce of the land on the day, unleavened bread and roasted grain.
12 Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
The manna stopped on the day after they ate the produce of the land. There was no longer manna for the people of Israel, but they ate the produce of the land of Canaan that year.
13 To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
When Joshua was near Jericho, he lifted up his eyes and looked, and behold, a man was standing in front of him; he had drawn his sword and it was in his hand. Joshua went to him and said, “Are you for us or for our enemies?”
14 Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
He said, “Neither. For I am the commander of the army of Yahweh. Now I have come.” Then Joshua lay facedown on the ground to worship and said to him, “What does my master say to his servant?”
15 Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.
The commander of Yahweh's army said to Joshua, “Take off your sandals from your feet, because the place you are standing is holy.” That is what Joshua did.

< Yoshuwa 5 >