< Yoshuwa 4 >

1 Da al’umma gaba ɗaya suka ƙetare Urdun, Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
And it came to pass, when all the people had quite passed over Jordan, that the LORD spoke to Joshua, saying,
2 “Ka zaɓi mutum goma sha biyu daga cikin mutane, ɗaya daga kowace kabila,
Take you twelve men from the people, from every tribe a man,
3 ka ce musu kowa yă ɗauki dutse ɗaya daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, ku kai su, ku ajiye a inda za ku sauka yau.”
And command ye them, saying, Take you hence out of the midst of Jordan, from the place where the priests' feet stood firm, twelve stones, and ye shall carry them over with you, and leave them in the lodging-place where ye shall lodge this night.
4 Sai Yoshuwa ya kira mutum goma sha biyu da ya zaɓa daga cikin Isra’ilawa, ɗaya daga kowace kabila
Then Joshua called the twelve men, whom he had prepared of the children of Israel, of every tribe a man:
5 ya ce musu, “Ku je tsakiyar Urdun inda akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku yake. Kowannenku yă ɗauki dutse ɗaya a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilan Isra’ila,
And Joshua said to them, Pass over before the ark of the LORD your God into the midst of Jordan, and take ye up every man of you a stone upon his shoulder, according to the number of the tribes of the children of Israel:
6 yă zama muku alama. Nan gaba in yaranku suka tambaye ku suka ce, ‘Mece ce ma’anar kasancewar duwatsun nan a nan?’
That this may be a sign among you, [that] when your children ask [their fathers] in time to come, saying, What [mean] ye by these stones?
7 Sai ku ce musu, ruwan Urdun ya yanke a gaban akwatin alkawari na Ubangiji, a lokacin da akwatin alkawarin ya ƙetare Urdun. Waɗannan duwatsu za su zama abin tuni ga Isra’ilawa har abada.”
Then ye shall answer them, That the waters of Jordan were cut off before the ark of the covenant of the LORD; when it passed over Jordan, the waters of Jordan were cut off: and these stones shall be for a memorial to the children of Israel for ever.
8 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Yoshuwa ya umarce su. Suka ɗauki duwatsu guda goma sha biyu bisa ga yawan kabilan Isra’ila, yadda Ubangiji ya gaya wa Yoshuwa; suka tafi da su masauƙinsu, a can suka ajiye su.
And the children of Israel did so as Joshua commanded, and took up twelve stones from the midst of Jordan, as the the LORD commanded Joshua, according to the number of the tribes of the children of Israel, and carried them over with them to the place where they lodged, and laid them down there.
9 Yoshuwa ya ɗora duwatsu goma sha biyun a tsakiyar Urdun daidai inda firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya. Suna nan a can har wa yau.
And Joshua set up twelve stones in the midst of Jordan, in the place where the feet of the priests who bore the ark of the covenant stood: and they are there to this day.
10 Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Yoshuwa yă gaya wa mutane, kamar yadda Musa ya ce Yoshuwa yă yi. Mutanen suka wuce da sauri.
For the priests who bore the ark stood in the midst of Jordan, until every thing was finished that the LORD commanded Joshua to speak to the people, according to all that Moses commanded Joshua: and the people hasted and passed over.
11 Sai da dukan mutanen suka wuce sa’an nan akwatin alkawari da firistoci suka sha gaba.
And it came to pass, when all the people had quite passed over, that the ark of the LORD passed over, and the priests in the presence of the people.
12 Mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse suka ƙetare da shirin yaƙi, suka wuce gaban Isra’ila kamar yadda Musa ya ce su yi.
And the children of Reuben, and the children of Gad, and half the tribe of Manasseh, passed over armed before the children of Israel, as Moses directed them:
13 Wajen mutum dubu arba’in shirye domin yaƙi, suka wuce a gaban Ubangiji zuwa filayen Yeriko.
About forty thousand prepared for war passed over before the LORD to battle, to the plains of Jericho.
14 A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Yoshuwa a gaban Isra’ilawa; suka kuma ba shi girma dukan kwanakin ransa, kamar yadda suka girmama Musa.
On that day the LORD magnified Joshua in the sight of all Israel, and they feared him, as they feared Moses, all the days of his life.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
And the LORD spoke to Joshua, saying,
16 “Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin Shaida su fito daga cikin Urdun.”
Command the priests that bear the ark of the testimony, that they come up out of Jordan.
17 Sai Yoshuwa ya umarci firistoci ya ce, “Ku fito daga cikin Urdun.”
Joshua therefore commanded the priests, saying, Come ye up out of Jordan.
18 Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
And it came to pass, when the priests that bore the ark of the covenant of the LORD had come up out of the midst of Jordan, [and] the soles of the priests' feet were lifted up upon the dry land, that the waters of Jordan returned to their place, and flowed over all its banks, as [they did] before.
19 A rana ta goma ga wata na farko, mutane suka haura daga Urdun suka sauka a Gilgal a gabashin iyakar Yeriko.
And the people came up out of Jordan on the tenth [day] of the first month, and encamped in Gilgal, in the east border of Jericho.
20 Sai Yoshuwa ya kafa duwatsu goma sha biyun nan da suka ɗauko daga Urdun.
And those twelve stones which they took out of Jordan, did Joshua set up in Gilgal.
21 Ya ce wa Isra’ilawa, “Nan gaba in yaranku suka tambayi iyayensu suka ce, ‘Mece ce ma’anar waɗannan duwatsun?’
And he spoke to the children of Israel, saying, When your children shall ask their fathers in time to come, saying, What [mean] these stones?
22 Ku ce musu, ‘Isra’ilawa sun ƙetare kogin Urdun a kan busasshiyar ƙasa.’
Then ye shall let your children know, saying, Israel came over this Jordan on dry land.
23 Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya yanke a gabanku, har sai da kuka gama wucewa, kamar yadda ya yi a Jan Teku, a lokacin da ya busar da shi a gabanmu har sai da muka gama wucewa.
For the LORD your God dried up the waters of Jordan from before you, until ye had passed over, as the LORD your God did to the Red sea, which he dried up from before us, until we had gone over:
24 Ya yi wannan ne domin dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji mai iko ne, domin kuma ku zama masu tsoron Ubangiji Allahnku.”
That all the people of the earth might know the hand of the LORD that it [is] mighty: that ye might fear the LORD your God for ever.

< Yoshuwa 4 >