< 1 Sama’ila 2 >

1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
And Hannah prayed, and said, My heart rejoiceth in the LORD, my horn is exalted in the LORD; my mouth is enlarged over my enemies; because I rejoice in thy salvation.
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
[There is] none holy as the LORD: for [there is] none besides thee: neither [is there] any rock like our God.
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
Talk no more so exceeding proudly; let [not] arrogance come out of your mouth: for the LORD [is] a God of knowledge, and by him actions are weighed.
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
The bows of the mighty men [are] broken, and they that stumbled are girded with strength.
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
[They that were] full have hired out themselves for bread; and [they that were] hungry ceased: so that the barren hath borne seven; and she that hath many children is become feeble.
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
The LORD killeth, and maketh alive: he bringeth down to the grave, and bringeth up. (Sheol h7585)
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
The LORD maketh poor, and maketh rich: he bringeth low, and lifteth up.
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
He raiseth the poor out of the dust, [and] lifteth the beggar from the dunghill, to set [them] among princes, and to make them inherit the throne of glory: for the pillars of the earth [are] the LORD'S, and he hath set the world upon them.
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
He will keep the feet of his saints, and the wicked shall be silent in darkness; for by strength shall no man prevail.
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
The adversaries of the LORD shall be broken to pieces; out of heaven shall he thunder upon them: the LORD shall judge the ends of the earth; and he shall give strength to his king, and exalt the horn of his anointed.
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
And Elkanah went to Ramah to his house. And the child ministered to the LORD before Eli the priest.
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
Now the sons of Eli [were] sons of Belial; they knew not the LORD.
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
And the priest's custom with the people [was], [that], when any man offered sacrifice, the priest's servant came, while the flesh was in seething, with a flesh-hook of three teeth in his hand;
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
And he struck [it] into the pan, or kettle, or caldron, or pot; all that the flesh-hook brought up the priest took for himself. So they did in Shiloh to all the Israelites that came thither.
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
Also before they burnt the fat, the priest's servant came, and said to the man that sacrificed, Give flesh to roast for the priest; for he will not have boiled flesh of thee, but raw.
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
And [if] any man said to him, Let them not fail to burn the fat presently, and [then] take [as much] as thy soul desireth; then he would answer him, [No]; but thou shalt give [it to me] now: and if not, I will take [it] by force.
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
Wherefore the sin of the young men was very great before the LORD: for men abhorred the offering of the LORD.
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
But Samuel ministered before the LORD, [being] a child, girded with a linen ephod.
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
Moreover his mother made him a little coat, and brought [it] to him from year to year, when she came up with her husband, to offer the yearly sacrifice.
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
And Eli blessed Elkanah and his wife, and said, The LORD give thee issue of this woman for the loan which is lent to the LORD. And they went to their own home.
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
And the LORD visited Hannah, so that she conceived, and bore three sons and two daughters. And the child Samuel grew before the LORD.
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
Now Eli was very old, and heard all that his sons did to all Israel; and how they lay with the women that assembled at the door of the tabernacle of the congregation.
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
And he said to them, Why do ye such things? for I hear of your evil dealings by all this people.
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
No, my sons; for [it is] no good report that I hear: ye make the LORD'S people to transgress.
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
If one man shall sin against another, the judge shall judge him: but if a man shall sin against the LORD, who shall entreat for him? Notwithstanding they hearkened not to the voice of their father, because the LORD would slay them.
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
And the child Samuel continued to grow, and was in favor both with the LORD, and also with men.
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
And there came a man of God to Eli, and said to him, Thus saith the LORD, Did I plainly appear to the house of thy father, when they were in Egypt in Pharaoh's house?
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
And did I choose him out of all the tribes of Israel [to be] my priest, to offer upon my altar, to burn incense, to wear an ephod before me? and did I give to the house of thy father all the offerings made by fire of the children of Israel?
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
Wherefore kick ye at my sacrifice and at my offering, which I have commanded [in my] habitation; and honorest thy sons above me, to make yourselves fat with the chiefest of all the offerings of Israel my people?
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
Wherefore the LORD God of Israel saith, I said indeed [that] thy house, and the house of thy father should walk before me for ever: but now the LORD saith, Be it far from me; for them that honor me I will honor, and they that despise me shall be lightly esteemed.
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
Behold, the days come, that I will cut off thy arm, and the arm of thy father's house, that there shall not be an old man in thy house.
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
And thou shalt see an enemy [in my] habitation, in all [the wealth] which [God] shall give Israel: and there shall not be an old man in thy house for ever.
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
And the man of thine, [whom] I shall not cut off from my altar, [shall be] to consume thy eyes, and to grieve thy heart: and all the increase of thy house shall die in the flower of their age.
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
And this [shall be] a sign to thee, that shall come upon thy two sons, on Hophni and Phinehas: in one day they shall die both of them.
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
And I will raise me up a faithful priest, [that] shall do according to [that] which [is] in my heart and in my mind: and I will build him a sure house; and he shall walk before my Anointed for ever.
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
And it shall come to pass, [that] every one that is left in thy house, shall come [and] crouch to him for a piece of silver and a morsel of bread, and shall say, Put me, I pray thee, into one of the priest's offices, that I may eat a piece of bread.

< 1 Sama’ila 2 >