< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then Eliphaz the Temanite answered,
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
“If someone ventures to talk with you, will you be grieved? But who can withhold himself from speaking?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Behold, you have instructed many, you have strengthened the weak hands.
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Your words have supported him who was falling, you have made the feeble knees firm.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
But now it has come to you, and you faint. It touches you, and you are troubled.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Isn’t your piety your confidence? Isn’t the integrity of your ways your hope?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
“Remember, now, who ever perished, being innocent? Or where were the upright cut off?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
According to what I have seen, those who plow iniquity and sow trouble, reap the same.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
By the breath of God they perish. By the blast of his anger are they consumed.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
The roaring of the lion, and the voice of the fierce lion, the teeth of the young lions, are broken.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
The old lion perishes for lack of prey. The cubs of the lioness are scattered abroad.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
“Now a thing was secretly brought to me. My ear received a whisper of it.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
In thoughts from the visions of the night, when deep sleep falls on men,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
fear came on me, and trembling, which made all my bones shake.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Then a spirit passed before my face. The hair of my flesh stood up.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
It stood still, but I couldn’t discern its appearance. A form was before my eyes. Silence, then I heard a voice, saying,
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
‘Shall mortal man be more just than God? Shall a man be more pure than his Maker?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Behold, he puts no trust in his servants. He charges his angels with error.
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
How much more those who dwell in houses of clay, whose foundation is in the dust, who are crushed before the moth!
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Between morning and evening they are destroyed. They perish forever without any regarding it.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Isn’t their tent cord plucked up within them? They die, and that without wisdom.’

< Ayuba 4 >