< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then Bildad the Shuhite answered,
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
“How long will you speak these things? Shall the words of your mouth be a mighty wind?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Does God pervert justice? Or does the Almighty pervert righteousness?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
If your children have sinned against him, he has delivered them into the hand of their disobedience.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
If you want to seek God diligently, make your supplication to the Almighty.
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
If you were pure and upright, surely now he would awaken for you, and make the habitation of your righteousness prosperous.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Though your beginning was small, yet your latter end would greatly increase.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
“Please inquire of past generations. Find out about the learning of their fathers.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
(For we are but of yesterday, and know nothing, because our days on earth are a shadow.)
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Shall they not teach you, tell you, and utter words out of their heart?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
“Can the papyrus grow up without mire? Can the rushes grow without water?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
While it is yet in its greenness, not cut down, it withers before any other reed.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
So are the paths of all who forget God. The hope of the godless man will perish,
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
whose confidence will break apart, whose trust is a spider’s web.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
He will lean on his house, but it will not stand. He will cling to it, but it will not endure.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
He is green before the sun. His shoots go out along his garden.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
His roots are wrapped around the rock pile. He sees the place of stones.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
If he is destroyed from his place, then it will deny him, saying, ‘I have not seen you.’
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Behold, this is the joy of his way. Out of the earth, others will spring.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
“Behold, God will not cast away a blameless man, neither will he uphold the evildoers.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
He will still fill your mouth with laughter, your lips with shouting.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Those who hate you will be clothed with shame. The tent of the wicked will be no more.”

< Ayuba 8 >