< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
욥이 대답하여 가로되
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
이런 말은 내가 많이 들었나니 너희는 다 번뇌케 하는 안위자로 구나
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
허망한 말이 어찌 끝이 있으랴 네가 무엇에 격동되어 이같이 대답하는고
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
나도 너희처럼 말할 수 있나니 가령 너희 마음이 내 마음 자리에 있다 하자 나도 말을 지어 너희를 치며 너희를 향하여 머리를 흔들 수 있느니라
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
그래도 입으로 너희를 강하게 하며 입술의 위로로 너희의 근심을 풀었으리라
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
내가 말하여도 내 근심이 풀리지 아니하나니 잠잠한들 어찌 평안하랴
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
이제 주께서 나를 곤고케 하시고 나의 무리를 패괴케 하셨나이다
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
주께서 나를 시들게 하셨으니 이는 나를 향하여 증거를 삼으심이라 나의 파리한 모양이 일어나서 대면하여 나의 죄를 증거하나이다
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
그는 진노하사 나를 찢고 군박하시며 나를 향하여 이를 갈고 대적이 되어 뾰족한 눈으로 나를 보시고
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
무리들은 나를 향하여 입을 벌리며 나를 천대하여 뺨을 치며 함께 모여 나를 대적하는구나
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
하나님이 나를 경건치 않은 자에게 붙이시며 악인의 손에 던지셨구나
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
내가 평안하더니 그가 나를 꺾으시며 내 목을 잡아던져 나를 부숴뜨리시며 나를 세워 과녁을 삼으시고
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
그 살로 나를 사방으로 쏘아 인정 없이 내 허리를 뚫고 내 쓸개로 땅에 흘러나오게 하시는구나
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
그가 나를 꺾고 다시 꺾고 용사 같이 내게 달려드시니
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
내가 굵은 베를 꿰어매어 내 피부에 덮고 내 뿔을 티끌에 더럽혔구나
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
내 얼굴은 울음으로 붉었고 내 눈꺼풀에는 죽음의 그늘이 있구나
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
그러나 내 손에는 포학이 없고 나의 기도는 정결하니라
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
땅아 내 피를 가리우지 말라 나의 부르짖음으로 쉴 곳이 없게 되기를 원하노라
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
지금 나의 증인이 하늘에 계시고 나의 보인이 높은 데 계시니라
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
나의 친구는 나를 조롱하나 내 눈은 하나님을 향하여 눈물을 흘리고
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
사람과 하나님 사이에와 인자와 그 이웃 사이에 변백하시기를 원하노니
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
수 년이 지나면 나는 돌아오지 못할 길로 갈 것임이니라

< Ayuba 16 >