< Malachie 1 >

1 La charge de la parole de l'Eternel contre Israël, par le moyen de Malachie.
Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
2 Je vous ai aimés, a dit l'Eternel; et vous avez dit: En quoi nous as-tu aimés? Esaü n'était-il pas frère de Jacob, dit l'Eternel? Or j'ai aimé Jacob;
“Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
3 Mais j'ai haï Esaü, et j'ai mis ses montagnes en désolation, et son héritage pour les dragons du désert.
amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
4 Que si Edom dit: Nous avons été appauvris, mais nous retournerons, et rebâtirons les lieux ruinés, l'Eternel des armées dit ainsi: Ils rebâtiront, mais je détruirai, et on les appellera: Pays de méchanceté, et le peuple contre lequel l'Eternel est indigné à toujours.
Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
5 Vos yeux le verront, et vous direz: L'Eternel se magnifie sur [ceux qui sont] aux frontières d'Israël.
Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
6 Le fils honore le père, et le serviteur son Seigneur; si donc je suis Père, où [est] l'honneur qui m'appartient? et si je suis Seigneur, où est la crainte [qu'on a] de moi? a dit l'Eternel des armées, à vous Sacrificateurs, qui méprisez mon Nom. Et vous avez dit: En quoi avons-nous méprisé ton Nom?
“Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
7 Vous offrez sur mon autel du pain souillé, et vous dites: En quoi t'avons-nous déshonoré? C'est en ce que vous dites: La table de l'Eternel est contemplative.
“Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
8 Et quand vous amenez une bête aveugle pour la sacrifier, n'y a-t-il point de mal [en cela?] Et quand vous l'amenez boiteuse ou malade, n'y a-t-il point de mal [en cela?] Présente-la à ton Gouverneur, t'en saura-t-il gré, ou te recevra-t-il favorablement? a dit l'Eternel des armées.
Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Maintenant donc suppliez le [Dieu] Fort, afin qu'il ait pitié de nous; cela [venant] de votre main, vous recevra-t-il favorablement? a dit l'Eternel des armées.
“To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
10 Qui est aussi celui d'entre vous qui ferme les portes? car n'est-ce pas en vain que vous faites brûler le feu sur mon autel? Je ne prends point de plaisir en vous, a dit l'Eternel des armées; et je n'aurai point pour agréable l'oblation de vos mains.
“Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 Mais depuis le soleil levant jusqu'au soleil couchant, mon Nom sera grand parmi les nations, et en tous lieux on offrira à mon Nom le parfum, et une oblation pure; car mon Nom sera grand parmi les nations, a dit l'Eternel des armées.
Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 Mais vous l'avez profané, en disant: La table de l'Eternel est souillée, elle et ce qui en revient; sa viande est méprisable.
“Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
13 Vous dites aussi: Voici, ô que de travail! et vous soufflez dessus, a dit l'Eternel des armées. Vous amenez ce qui a été dérobé, ce qui est boiteux, et malade, vous l'amenez, dis-je, pour m'être offert. Accepterai-je cela de vos mains, a dit l'Eternel?
Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
14 C'est pourquoi, maudit soit l'homme trompeur, qui ayant un mâle en son troupeau, et faisant un vœu, sacrifie à l'Eternel ce qui est défectueux; car je suis un grand Roi, a dit l'Eternel des armées, et mon Nom est redouté parmi les nations.
“La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.

< Malachie 1 >