< Malachie 2 >

1 Or c'est maintenant à vous, Sacrificateurs, que s'adresse ce commandement:
“Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
2 Si vous n'écoutez point, et que vous ne preniez point à cœur de donner gloire à mon Nom, dit l'Eternel des armées, j'enverrai sur vous la malédiction, et je maudirai vos bénédictions; et [déjà] même je les ai maudites, parce que vous ne prenez point cela à cœur.
In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
3 Voici, je m'en vais tancer rudement votre postérité, et je répandrai la fiente [de vos victimes] sur vos visages, la fiente, [dis-je], de vos solennités; et elle vous emportera.
“Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
4 Alors vous saurez que je vous avais adressé ce commandement, que mon alliance fût avec Lévi; a dit l'Eternel des armées.
Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 Mon alliance de vie et de paix était avec lui; et je les lui ai données, afin qu'il me révérât; et il m'a révéré, et a été effrayé de la présence de mon Nom.
“Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
6 La Loi de vérité a été dans sa bouche, et il ne s'est point trouvé de perversité dans ses lèvres; il a marché avec moi dans la paix et dans la droiture, et il en a détourné plusieurs de l'iniquité.
Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
7 Car les lèvres du Sacrificateur gardaient la science, et on recherchait la Loi de sa bouche, parce qu'il était le messager de l'Eternel des armées.
“Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
8 Mais vous vous êtes retirés de ce chemin-là, vous avez fait broncher plusieurs dans la Loi, et vous avez corrompu l'alliance de Lévi, a dit l'Eternel des armées.
Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 C'est pourquoi je vous ai rendus méprisables et abjects à tout le peuple; car vous ne tenez point mes chemins, et vous avez égard à l'apparence des personnes en la Loi.
“Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
10 N'avons-nous pas tous un même Père? Un seul [Dieu] Fort ne nous a-t-il pas créés? Pourquoi [donc] chacun agit-il perfidement contre son frère, en violant l'alliance de nos pères?
Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
11 Juda a agi perfidement, et on a commis abomination dans Israël, et dans Jérusalem; car Juda a profané la sainteté de l'Eternel, qui l'aimait, et s'est marié à la fille d'un dieu étranger.
Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
12 L'Eternel retranchera des tabernacles de Jacob quiconque aura fait cette chose-là, tant celui qui réveille que celui qui répond, et que celui qui présente l’oblation à l'Eternel des armées.
Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
13 Et voici une autre chose que vous faites: Vous couvrez l'autel de l'Eternel de larmes, de plaintes, et de gémissements, de sorte que je ne regarde plus à l'oblation, et que je ne prends [rien] à gré de ce qui vient de vos mains.
Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
14 Et vous dites: Pourquoi? C'est parce que l'Eternel est intervenu comme témoin entre toi et la femme de ta jeunesse, contre laquelle tu agis perfidement; et toutefois elle est ta compagne, et la femme qui t'a été accordée.
Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
15 Or il n'en a fait qu'un; et néanmoins il y avait en lui abondance d'esprit. Mais pourquoi [n'en a-t-il fait] qu'un? C'est parce qu'il cherchait une postérité de Dieu. Gardez-vous donc dans votre esprit; et quant à la femme de ta jeunesse, [prenez garde] qu'on n'agisse point perfidement [avec] elle.
Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
16 Car l'Eternel le Dieu d'Israël a dit qu'il hait qu'on la renvoie. Mais on couvre la violence sous sa robe, a dit l'Eternel des armées. Gardez-vous donc dans votre esprit, et n'agissez point en perfides.
“Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
17 Vous avez travaillé l'Eternel par vos paroles; vous avez dit: En quoi l'avons-nous travaillé? C'est quand vous dites: Quiconque fait du mal plaît à l'Eternel, et il prend plaisir à de telles gens. Autrement où est le Dieu du jugement?
Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”

< Malachie 2 >