< 1 Chroniques 10 >

1 Or les Philistins combattirent contre Israël, et ceux d'Israël s'enfuirent devant les Philistins, et tombèrent blessés à mort en la montagne de Guilboah.
To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
2 Et les Philistins poursuivirent et atteignirent Saül et ses fils, et tuèrent Jonathan, Abinadab et Malki-suah, les fils de Saül.
Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
3 Et le combat se renforça contre Saül, de sorte que ceux qui tiraient de l'arc le trouvèrent, et il eut peur de ces archers.
Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
4 Alors Saül dit à celui qui portait ses armes: Tire ton épée, et m'en transperce, de peur que ces incirconcis ne viennent, et ne fassent de moi selon leur volonté; mais celui qui portait ses armes ne le voulut point faire; parce qu'il craignait beaucoup. Saül donc prit [son] épée, et se jeta dessus.
Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
5 Alors celui qui portait les armes de Saül, ayant vu que Saül était mort, se jeta aussi sur son épée, et mourut.
Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
6 Ainsi mourut Saül, et ses trois fils; et tous ses gens moururent avec lui.
Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
7 Et tous ceux d'Israël, qui étaient dans la vallée, ayant vu qu'ils s'en étaient fuis, et que Saül et ses fils étaient morts, abandonnèrent leurs villes, et s'enfuirent, de sorte que les Philistins y entrèrent, et y habitèrent.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
8 Or il arriva que dès le lendemain les Philistins vinrent pour dépouiller les morts, et ils trouvèrent Saül et ses fils étendus en la montagne de Guilboah.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
9 Et l'ayant dépouillé, ils lui ôtèrent la tête, et ses armes, et les envoyèrent au pays des Philistins tout à l'environ, pour en faire savoir les nouvelles à leurs dieux, et au peuple.
Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
10 Ils mirent ses armes au temple de leur dieu, et ils attachèrent sa tête en la maison de Dagon.
Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
11 Or tous ceux de Jabés de Galaad ayant appris tout ce que les Philistins avaient fait à Saül,
Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
12 Tous les vaillants hommes [d'entr'eux] se levèrent, et enlevèrent le corps de Saül, et les corps de ses fils, et les apportèrent à Jabés, et ils ensevelirent leurs os sous un chêne à Jabés, et jeûnèrent pendant sept jours.
sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
13 Saül donc mourut pour le crime qu'il avait commis contre l'Eternel, en ce qu'il n'avait point gardé la parole de l'Eternel, et qu'il avait même consulté l'esprit de Python pour [savoir ce qui lui devait arriver].
Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
14 Il ne s'était point adressé à l'Eternel; c'est pourquoi [l'Eternel] le fit mourir, et transporta le Royaume à David fils d'Isaï.
bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.

< 1 Chroniques 10 >