< 2 Rois 1 >

1 Or après la mort d'Achab Moab se rebella contre Israël.
Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
2 Et Achazia tomba par le treillis de sa chambre haute qui était à Samarie, et en fut malade; et il envoya des messagers, et leur dit: Allez consulter Bahal-zébub, dieu de Hékron, [pour savoir] si je relèverai de cette maladie.
Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
3 Mais l'Ange de l'Eternel parla à Elie Tisbite, en disant: Lève-toi, monte au devant des messagers du Roi de Samarie, et leur dis: N'y [a-t-il] point de Dieu en Israël, que vous alliez consulter Bahal-zébub, dieu de Hékron?
Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
4 C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel: Tu ne descendras point du lit sur lequel tu es monté, mais certainement tu mourras. Cela dit, Elie s'en alla.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
5 Et les messagers s'en retournèrent vers Achazia, et il leur dit: Pourquoi êtes-vous revenus?
Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
6 Et ils lui répondirent: Un homme est monté au-devant de nous, qui nous a dit: Allez, retournez vous-en vers le Roi qui vous a envoyés, et dites-lui: Ainsi a dit l'Eternel: N'y a-t-il point de Dieu en Israël, que tu envoies consulter Bahal-zébub dieu de Hékron? A cause de cela tu ne descendras point du lit sur lequel tu es monté, mais certainement tu mourras.
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
7 Et il leur dit: Comment était fait cet homme qui est monté au devant de vous, et qui vous a dit ces paroles?
Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
8 Et ils lui répondirent: C'est un homme vêtu de poil, qui a une ceinture de cuir, ceinte sur ses reins; et il dit: C'est Elie Tisbite.
Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
9 Alors il envoya vers lui un capitaine de cinquante hommes, avec sa cinquantaine, lequel monta vers lui. Or voilà, il se tenait au sommet d'une montagne, et [ce capitaine] lui dit: Homme de Dieu, le Roi a dit que tu aies à descendre.
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
10 Mais Elie répondit, et dit au capitaine de la cinquantaine: Si je suis un homme de Dieu, que le feu descende des cieux, et te consume, toi et ta cinquantaine! Et le feu descendit des cieux, et le consuma, lui et sa cinquantaine.
Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
11 Et [Achazia] envoya encore un autre capitaine de cinquante hommes avec sa cinquantaine, qui prit la parole, et lui dit: Homme de Dieu, ainsi a dit le Roi: Hâte-toi de descendre.
Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
12 Mais Elie répondit, et leur dit: Si je suis un homme de Dieu, que le feu descende des cieux et te consume, toi et ta cinquantaine; et le feu de Dieu descendit des cieux, et le consuma, lui et sa cinquantaine.
Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
13 Et [Achazia] envoya encore un capitaine d'une troisième cinquantaine avec sa cinquantaine, et ce troisième capitaine de cinquante hommes monta, et vint, et se courba sur ses genoux devant Elie, et le supplia, et lui dit: Homme de Dieu, je te prie que tu fasses cas de ma vie, et de la vie de ces cinquante hommes tes serviteurs.
Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
14 Voilà, le feu est descendu des cieux, et a consumé les deux premiers capitaines de cinquante hommes, avec leurs cinquantaines; mais maintenant [je te prie], que tu fasses cas de ma vie.
Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
15 Et l'Ange de l'Eternel dit à Elie: Descends avec lui, n'aie point peur de lui. Il se leva donc, et descendit avec lui vers le Roi,
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
16 Et lui dit: Ainsi a dit l'Eternel: Parce que tu as envoyé des messagers pour consulter Bahal-zébub dieu de Hékron, comme s'il n'y avait point de Dieu en Israël, pour consulter sa parole: tu ne descendras point du lit sur lequel tu es monté, mais certainement tu mourras.
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
17 Il mourut donc, selon la parole de l'Eternel, qu'Elie avait prononcée; et Joram commença à régner en sa place, la seconde année de Joram, fils de Josaphat, Roi de Juda, parce qu'Achazia n'avait point de fils.
Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
18 Le reste des faits d'Achazia, lesquels il fit, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois d'Israël?
Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?

< 2 Rois 1 >