< Psaumes 35 >

1 De David. Seigneur, juge ceux qui me nuisent; combats ceux qui me font la guerre.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Prends tes armes et ton bouclier; lève-toi à mon aide.
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Tire le glaive et ferme la voie à ceux qui me poursuivent; dis à mon âme: Je suis ton salut.
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Que ceux qui en veulent à ma vie soient confondus et frappés de crainte; que ceux qui pensent à mal contre moi soient confondus et mis en fuite.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 Qu'ils soient comme la poussière devant la face des vents; que l'ange du Seigneur les arrête.
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 Que leur voie soit ténébreuse et glissante; que l'ange du Seigneur les poursuive.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 Parce que sans motif ils ont caché pour moi la mort dans un piège, et que sans motif ils ont fait des outrages à mon âme:
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 Qu'un filet inconnu tombe sur eux; que les lacs qu'ils ont cachés les prennent; qu'ils trébuchent dans leurs propres pièges.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 Et mon âme mettra sa joie dans le Seigneur; elle se délectera dans son salut.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 Tous mes os diront: Seigneur qui est semblable à toi? Tu sauves l'indigent de mains plus fortes que lui; tu protèges le mendiant et le pauvre contre ceux qui le pillent.
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 De faux témoins se sont levés, et ils m'ont questionné sur ce que je ne savais pas.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 Ils me rendaient le mal pour le bien; ils ont desséché ma vie.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 Et moi, tandis qu'ils me tourmentaient, je me suis couvert d'un cilice; j'ai mortifié mon âme par le jeûne, et ma prière retournera en mon sein.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 Je me complaisais en eux comme en un ami ou en mon frère; je m'étais humilié comme si j'eusse été dans le deuil et la tristesse.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 Et ils se réjouissaient contre moi, et ils s'assemblaient et réunissaient leurs forces contre moi, et je n'en savais rien; ils ont été dissipés, mais non contrits;
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 Ils m'ont tenté; ils ont ricané avec grand mépris; ils ont grincé des dents sur moi.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Seigneur, quand regarderas-tu vers moi? Sauve mon âme de leur malice; délivre des lions mon âme abandonnée.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 Je te rendrai gloire en une église nombreuse; je te louerai au milieu d'un grand peuple.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Que ne je vois point la joie de ceux qui m'attaquent injustement, qui me haïssent sans raison et me regardent d'un œil méprisant.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 Ils m'ont parlé pacifiquement; mais dans leur colère ils songeaient à me tromper.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 Ils ont dilaté contre moi leur bouche, et ils ont dit: Bien, bien, nos yeux ont vu.
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Toi aussi, Seigneur, tu as vu; ne gardez pas le silence, Seigneur; ne t'éloigne pas de moi.
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Lève-toi, Seigneur, applique-toi à mon jugement; mon Seigneur et mon Dieu, sois attentif à ma cause.
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Juge-moi, Seigneur, selon ta justice, mon Seigneur et mon Dieu, et qu'ils ne fassent pas de moi leur joie;
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 Qu'ils ne disent point en leur cœur: Bien, cela plaît à notre âme; qu'ils ne disent point: Nous l'avons dévoré.
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Que ceux qui se sont réjouis de mes maux soient confondus et honteux; que ceux qui ont parlé contre moi en se gonflant d'orgueil, soient enveloppés de crainte et de confusion.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 Que ceux qui veulent ma justification soient dans la joie; qu'ils tressaillent d'allégresse; qu'ils ne cessent de dire: Dieu soit glorifié, et ceux qui désirent la paix de son serviteur.
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 Et ma langue célébrera ta justice; elle chantera chaque jour tes louanges.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.

< Psaumes 35 >