< Proverbes 1 >

1 Proverbes de Salomon, fils de David, qui régna en Israël,
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 pour faire connaître la sagesse et la discipline; pour apprendre les paroles de la prudence;
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 pour montrer les artifices des discours; pour enseigner vraiment la justice, pour instruire à juger avec rectitude;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 pour donner aux innocents la sagacité, aux jeunes gens la doctrine et l'intelligence.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Car le sage qui les aura ouïs sera plus sage, et l'homme entendu saura l'art de gouverner.
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 Il pénétrera la parabole et le sens voilé, et les paroles des sages, et leurs énigmes.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 La crainte du Seigneur est le commencement de la sagesse; la prudence est bonne à tous ceux qui la mettent en pratique; la piété envers Dieu est le principe de la sagesse; les insensés méprisent la sagesse et la doctrine.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Écoute, mon fils, les instructions de ton père, et ne repousse pas la loi de ta mère
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 et tu ajouteras une couronne de grâces à ta tête, et à ton cou un collier d'or.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Mon fils, prends garde que les impies ne t'égarent; ne leur donne pas ton consentement.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 S'ils te convient, disant: Viens avec nous, prends ta part du sang; cachons en terre injustement l'homme juste;
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 engloutissons-le tout vivant, comme dans l'enfer, et effaçons de la terre tout souvenir de lui. (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 Emparons-nous de ses richesses les plus précieuses, et remplissons nos demeures de ses dépouilles.
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Mets ta part avec la nôtre; faisons tous bourse commune et n'ayons qu'un trésor.
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 Mon fils, ne vas pas en leur voie; éloigne ton pied de leurs sentiers;
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 Car leurs pieds courent au mal, ils se hâtent pour répandre le sang.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 car ce n'est pas vainement qu'on tend des filets aux oiseaux.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 Mais ceux qui participent à un meurtre thésaurisent pour eux des malheurs; et la chute des pervers est funeste.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Telles sont les voies de tous les ouvriers d'iniquité; par leur impiété, ils détruisent leur propre vie.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 La Sagesse chante dans les rues; elle parle librement au milieu des places.
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 Et du haut des remparts elle crie comme un héraut, et elle s'assied devant les portes des riches; et aux portes de la cité, pleine d'assurance, elle dit:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 Tant que les innocents s'attacheront à la justice, ils ne seront point humiliés; quant aux insensés, pleins de désirs honteux, devenus impies, ils haïssent la science,
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 et sont exposés aux opprobres. Voilà que je vais proférer pour vous les paroles de mon esprit; je vais vous enseigner mes discours.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 J'ai appelé, et vous n'avez point obéi; j'ai parlé longuement, et vous n'étiez pas attentifs;
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 mais vous avez mis à néant mes conseils, et vous avez été rebelles à mes réprimandes.
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 Aussi moi je rirai au jour de votre perte, et je me réjouirai quand viendra votre ruine,
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 et quand soudain le trouble fondra sur vous, et que votre catastrophe sera là comme une tempête, et quand viendra sur vous la tribulation et l'oppression, et enfin la mort.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Car alors vous m'invoquerez; mais moi je ne vous écouterai point; les méchants me chercheront, et ils ne me trouveront pas.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Car ils haïssent la Sagesse; et ils n'ont point choisi de préférence la parole du Seigneur.
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 Et ils n'ont point voulu être attentifs à mes conseils; et ils se sont raillés de mes reproches.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Aussi mangeront-ils les fruits de leurs voies; et ils se rassasieront de leur propre impiété.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Car ils seront mis à mort, pour avoir fait tort aux petits; et l'examen de leur cause perdra les impies.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 Tandis que celui qui m'écoute s'abritera sous l'espérance, et se reposera sans avoir à craindre aucun mal.
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Proverbes 1 >