+ Genèse 1 >

1 Au commencement Dieu créa le ciel et la terre.
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2 Or la terre était invisible et vide; les ténèbres étaient au-dessus de l'abîme, et l'Esprit de Dieu était porté sur les eaux.
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3 Et Dieu dit: Soit la lumière, et la lumière fut.
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
4 Dieu vit que la lumière était bonne, et il sépara la lumière des ténèbres.
Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5 Dieu appela la lumière jour; il appela nuit les ténèbres. Et il y eut un soir, et il y eut un matin; un jour.
Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
6 Dieu dit ensuite: Qu'il y ait un firmament au milieu des eaux; qu'il sépare les eaux des eaux; et il en fut ainsi.
Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
7 Dieu créa le firmament, il sépara les eaux qui étaient au-dessus du firmament, des eaux qui étaient au-dessous du firmament.
Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
8 Il appela le firmament ciel. Et Dieu vit que cela était bien. Et il y eut un soir, et il y eut un matin, et ce fut un deuxième jour.
Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
9 Après quoi Dieu dit: Que les eaux, au-dessous du ciel, soient réunies en un seul amas, et que l'aride apparaisse. Et il en fut ainsi: les eaux, au- dessous du ciel, furent réunies en un seul amas, et l'aride apparut.
Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
10 Dieu appela l'aride terre; il appela mers l'amas des eaux. Et Dieu vit que cela était bien.
Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
11 Et Dieu dit: Que la terre produise des plantes herbacées, portant semence selon les espèces et les similitudes, et des arbres fertiles en fruits, qui aient en eux les semences propres à chaque espèce sur la terre. Et il en fut ainsi:
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
12 La terre produisit des plantes herbacées, portant semence selon les espèces et les similitudes, et des arbres fertiles en fruits ayant en eux les semences propres à chaque espèce sur la terre. Et Dieu vit que cela était bien.
Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
13 Et il y eut un soir, et il y eut un matin, et ce fut un troisième jour.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
14 Dieu dit ensuite: Que des luminaires soient dans le firmament du ciel, pour luire sur la terre et séparer les jours et les nuits; qu'ils soient les signes des temps et des jours et des années;
Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
15 Qu'ils brillent au firmament du ciel, pour éclairer la surface de la terre. Et il en fut ainsi:
bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
16 Dieu créa les deux grands luminaires: le plus grand luminaire pour présider aux jours, le luminaire le plus petit pour présider aux nuits. Il créa les étoiles,
Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
17 Qu'il plaça dans le firmament du ciel pour éclairer la surface de la terre,
Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
18 Présider aux jours et aux nuits, et séparer la lumière des ténèbres. Et Dieu vit que cela était bien.
su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
19 Et il y eut un soir, et il y eut un matin, et ce fut un quatrième jour.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
20 Et Dieu dit: Que les eaux produisent des reptiles, âmes vivantes, et des oiseaux volant sur la terre, sous le firmament du ciel. Et il en fut ainsi:
Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
21 Dieu créa les grands poissons, et tout reptile (âme vivante) que les eaux produisirent par espèces. Il créa tous les oiseaux ailés par espèces. Et Dieu vit que cela était bien.
Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
22 Puis Dieu les bénit, disant: Croissez et multipliez, remplissez les eaux des mers; et que les oiseaux multiplient sur la terre.
Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
23 Et il y eut un soir, et il y eut un matin, et ce fut un cinquième jour.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
24 Dieu dit ensuite: Que la terre produise des âmes vivantes, selon les espèces: quadrupèdes, reptiles, bêtes fauves de la terre, par espèces. Et il en fut ainsi:
Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
25 Dieu créa les bêtes fauves de la terre, par espèces, les bestiaux selon leurs espèces, et tous les reptiles de la terre par espèces. Et Dieu vit que cela était bien.
Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
26 Alors Dieu dit: Créons l'homme à notre image et ressemblance, qu'il ait tout pouvoir sur les poissons de la mer, sur les oiseaux du ciel, et sur les bestiaux, et sur toute la terre, et sur les reptiles se traînant à terre.
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
27 Et Dieu créa l'homme; il le créa à l'image de Dieu; il les créa mâle et femelle.
Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
28 Et Dieu les bénit, disant: Croissez et multipliez, remplissez la terre, et dominez sur elle; soyez maîtres des poissons de la mer, et des oiseaux du ciel, et de tous les bestiaux, et de toute la terre, et de tous les reptiles qui se traînent à terre.
Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
29 Voyez, dit Dieu, je vous donne toutes les plantes à semence qui germent à la surface de la terre; que tous les arbres qui portent des fruits à semence soient à vous, pour être votre nourriture.
Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
30 Que toutes les bêtes fauves de la terre, tous les oiseaux du ciel, tous les reptiles qui se traînent à terre, et ont en eux une âme vivante, aient pour nourriture toute herbe verdoyante. Et il en fut ainsi.
Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
31 Et Dieu regarda toutes les choses qu'il avait créées; et les trouva excellemment bonnes. Et il y eut un soir, et il y eut un matin, et ce fut un sixième jour.
Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.

+ Genèse 1 >