< Exode 1 >

1 Voici les noms des fils d'Israël venus en Égypte avec Jacob, leur père, et qui y entrèrent chacun avec toute sa famille:
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
2 Ruben, Siméon, Lévi, Juda,
Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
3 Issachar, Zabulon, Benjamin,
Issakar, Zebulun da Benyamin;
4 Dan et Nephthali, Gad et Aser.
Dan da Naftali; Gad da Asher.
5 Joseph, de son côté, était déjà en Égypte; or, il y avait en tout soixante-quinze âmes provenant de Jacob.
Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
6 Et Joseph mourut, ainsi que tous ses frères, et toute cette génération.
Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
7 Puis, les fils d'Israël crûrent et se multiplièrent; ils se répandirent, et ils se fortifièrent beaucoup, beaucoup ils semblaient pulluler de la terre.
amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
8 Mais un autre roi s'éleva sur l'Égypte, qui ne connaissait pas Joseph.
Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
9 Et il dit à sa nation: Voilà que cette race des fils d'Israël forme une multitude immense et plus forte que nous.
Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
10 Allons donc, et employons contre eux l'artifice, de peur qu'ils ne se multiplient encore; car si une guerre survenait, ils se joindraient aux ennemis, et, nous ayant vaincus, ils sortiraient de cette contrée.
Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
11 En conséquence, il établit sur eux des intendants des travaux, afin qu'ils les épuisassent par le labeur; et ils bâtirent des villes fortes au Pharaon: Pitho, Rhamessès et On, aujourd'hui Héliopolis.
Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
12 Mais plus on les opprimait, plus ils devenaient nombreux, plus leur force devenait immense, immense; et les Égyptiens avaient en abomination les fils d'Israël.
Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
13 Les Égyptiens opprimaient donc par la force les fils d'Israël.
ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
14 Et ils affligeaient leur vie par de durs travaux, par l'argile, par la brique, par le labeur des champs; et ils les asservissaient par la violence à tous ces travaux.
Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
15 Alors, le roi des Égyptiens parla aux sages-femmes des Hébreux qui s'appelaient: la première, Séphora, la seconde, Phua.
Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
16 Et il dit: Lorsque vous accoucherez des femmes d'Hébreux, et qu'elles auront enfanté, si c'est un garçon, tuez-le; si c'est une fille, conservez-la.
“Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
17 Mais les sages-femmes craignirent Dieu, et n'exécutèrent point les ordres du roi d'Égypte; elles laissèrent vivre les enfants mâles.
Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
18 Alors, le roi d'Égypte appela les sages-femmes, et leur dit: Pourquoi agissez-vous de la sorte, et laissez-vous vivre les enfants mâles?
Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
19 Et les sages-femmes dirent au Pharaon: Les femmes des Hébreux ne sont pas comme les Égyptiennes; avant l'arrivée des sages-femmes, elles enfantent, et l'accouchement est fait.
Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
20 Et Dieu fit du bien aux sages-femmes; et le peuple se multiplia et se fortifia beaucoup.
Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
21 Et parce que les sages-femmes avaient eu la crainte de Dieu, elles se firent de bonnes maisons.
Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
22 Le Pharaon donna aussi ses ordres à son peuple, disant: Tout enfant mâle qui naîtra aux Hébreux, jetez-le dans le fleuve; et laissez vivre toutes les filles.
Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”

< Exode 1 >