< 1 Chroniques 26 >

1 Ceux à qui les portes furent distribuées, étaient les fils de Coré, Mosellamia, de la famille d'Asaph.
Ɓangarorin Matsaran Ƙofofi su ne, Daga Korayawa, Meshelemiya ɗan Kore, ɗaya daga cikin’ya’yan Asaf maza.
2 Et les fils de Mosellamia: Zacharie le premier-né, Jadiel le second, Zabadie le troisième, Jénuel le quatrième,
Meshelemiya yana da’ya’ya maza. Zakariya ɗan fari, Yediyayel na biyu, Zebadiya na uku, Yatniyel na huɗu,
3 Jolam le cinquième, Jonathan le sixième, Elionai le septième, Abdedom le huitième.
Elam na biyar, Yehohanan na shida da Eliyehoyenai na bakwai.
4 Et les fils d'Abdedom: Samaias le premier-né, Jozabath le second, Joath le troisième, Sachar le quatrième, Nathanaél le cinquième,
Obed-Edom shi ma yana da’ya’ya maza. Shemahiya ɗan fari, Yehozabad na biyu, Yowa na uku, Sakar na huɗu Netanel na biyar,
5 Amiel le sixième, Issachar le septième, Phelathi le huitième; car Dieu l'avait béni.
Ammiyel na shida, Issakar na bakwai da Feyuletai na takwas. (Gama Allah ya albarkace Obed-Edom.)
6 Et à son premier fils Samaïas, des fils naquirent, et furent chefs dans leur famille, parce qu'ils étaient forts
Ɗan Obed-Edom, wato, Shemahiya shi ma yana da’ya’ya maza, waɗanda suke shugabanni a cikin iyalin mahaifinsu, gama su jarumawa ne ƙwarai.
7 Fils de Samaï: Otbni, Raphaël, Obed, Elzabath, Achiud, tous hommes forts, Elia, Sabachias et Isbacom.
’Ya’yan Shemahiya maza su ne, Otni, Rafayel, Obed da Elzabad; danginsa Elihu da Shemahiya su ma jarumawa ne.
8 Tous issus d'Abdedom; eux, et leurs fils et leurs frères, remplissant avec énergie leurs fonctions, au nombre de soixante-deux, issus d'Abdedom.
Ɗaukan waɗannan zuriyar Obed-Edom ne; su da’ya’yansu maza da danginsu, jarumawa ne masu ƙarfin yin aiki. Zuriyar Obed-Edom, mutum 62 ne duka.
9 Mosellemia avait dix-huit fils et frères, tous hommes forts.
Meshelemiya yana da’ya’ya maza da kuma’yan’uwa, waɗanda jarumawa ne, su 18 ne duka.
10 Et les fils d'Osa, issu de Mérari, et qui n'était pas le premier-né, commandaient ce service; son père lui donna le commandement de la deuxième division.
Hosa dangin Merari yana da’ya’ya maza. Shimri na fari (ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, mahaifinsa ya sa shi na fari),
11 Helcias venait après lui, Tablé était le troisième, Zacharie le quatrième; les fils et les frères d'Osa étaient en tout: treize.
Hilkiya ne na biyu, Tabaliya ne na uku sai kuma Zakariya na huɗu.’Ya’ya da dangin Hosa su 13 ne duka.
12 C'est entre eux que furent partagées les portes; chefs énergiques, servant avec autant de zèle que leurs frères, employés dans l'intérieur du temple.
Waɗannan ɓangarori na matsaran ƙofofi, ta wurin manyansu, suna da ayyukan yin hidima a haikalin Ubangiji, kamar yadda danginsu suke da shi.
13 Et ils tirèrent au sort les portes où ils devaient être placés, après qu'on les eut classés, selon leur plus ou moins de force, par familles paternelles.
Aka jefa ƙuri’u don kowace ƙofa bisa ga iyalansu, ƙarami da babba.
14 Le sort désigna, pour la porte orientale, Sélémie et Zacharie; ensuite, les fils de Soaz, issu de Melchia, agitèrent les sorts, et celui de la porte du nord sortit.
Ƙuri’a don Ƙofar Gabas ta fāɗo a kan Shelemiya. Sai aka jefa ƙuri’u don ɗansa Zakariya, mai ba da shawara mai ma’ana, sai ƙuri’a ta ƙofar arewa ta fāɗo a kansa.
15 Abdedom eut la porte du midi, en face de la maison d'Esephim.
Ƙuri’a don Ƙofar Kudu ta fāɗo a kan Obed-Edom, ƙuri’a don ɗakin ajiya kuwa ta fāɗo a kan’ya’yansa maza.
16 Osa eut la seconde porte du côté de l'orient, après celle qui mène au vestibule des degrés; un garde vis-à-vis l'autre garde.
Ƙuri’u don Ƙofar Yamma da kuma Ƙofar Shalleket a hanyar bisa suka fāɗo a kan Shuffim da Hosa. Aikin tsaro bisa ga mai tsaro.
17 Il y avait chaque jour six hommes à la porte orientale, quatre à celle du nord, quatre à celle du midi et deux à Esephim,
Akwai Lawiyawa shida da suke tsaron ƙofar gabas, huɗu a ƙofar kudu, huɗu kuma a ƙofar arewa, biyu-biyu suke tsaron ɗakunan ajiya.
18 Pour la relève, du côté du couchant quatre et deux à l'entrée du chemin.
Game da filin waje ta yamma kuwa, akwai masu tsaro huɗu a hanya da kuma biyu a filin kansa.
19 Les portes étaient ainsi distribuées entre les fils dé Coré et ceux de Mérari.
Waɗannan su ne ɓangarori na matsaran ƙofofi waɗanda suke zuriyar Kora da Merari.
20 Et des lévites, leurs frères, gardaient le trésor de la demeure du Seigneur et le trésor des consécrations.
’Yan’uwansu Lawiyawa kuwa su ne suke lura da ma’ajin gidan Allah da kuma baitulmali don kayayyakin da aka keɓe.
21 Ceux-là étaient fils de Ladan; ils étaient issus des fils de Gerson; les chefs des familles provenaient de Ladan, le fils de Ladan le Gersonite était Jehiel.
Ladan ɗan Gershon ne, kuma kaka ga iyalai masu yawa, har ma da iyalin ɗansa Yehiyeli,
22 Zethom et Johel, son frère, fils de Jehiel, étaient intendants du trésor de la demeure du Seigneur,
’ya’yan Yehiyeli maza su ne, Zetam da ɗan’uwansa Yowel. Su ne suke kula da ma’ajin haikalin Ubangiji.
23 Avec les familles d'Amram, d'Issaar, d'Hébron et d'Oziel.
Daga zuriyar Amram, Izhar, mutanen Hebron da kuma Uzziyel, su ma aka ba su aiki.
24 Subael, issu de Gersam, fils de Moïse, était aussi intendant des trésors.
Shebuwel ɗan Gershom, daga zuriyar Musa, shi ne babban jami’i mai lura da baitulmali.
25 Or, Eliézer, l'un de ses proches, eut pour fils Rabias, de qui descendirent: Josias, Joram, Zéchri et Salomoth.
Danginsa na wajen Eliyezer su ne, Rehabiya, Yeshahiya, Yoram, Zikri da Shelomit.
26 Ce Salomoth et ses frères eurent l'intendance de tous les trésors saints, que consacrèrent le roi David et les chefs de familles paternelles, commandants de mille hommes, ou centeniers, ou princes de l'armée;
Shelomit da danginsa su ne suke lura da dukan baitulmali don kayayyakin da Sarki Dawuda ya keɓe, ta wajen kawunan iyalai waɗanda suke shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, da kuma wajen sauran shugabannin mayaƙa.
27 C'étaient les choses qu'ils avaient enlevées des villes prises sur l'ennemi, et consacrées pour subvenir aux frais de construction du temple de Dieu.
Sun keɓe waɗansu ganimar da aka kwaso a yaƙi don gyaran haikalin Ubangiji.
28 Ainsi, tout ce qu'avait consacré Samuel le prophète; Saül, fils de Cis; Abner, fils de Ner; Joab, fils de Servie, fut confié à Salomoth et à ses frères.
Shelomit da’yan’uwansa suka lura da dukan abubuwan da annabi Sama’ila da Shawulu ɗan Kish, da Abner ɗan Ner, da Yowab ɗan Zeruhiya suka keɓe.
29 Honnias, issu d'Isaar, et ses fils, furent chargés de fonctions extérieures en Israël; ils étaient scribes et juges.
Daga mutanen Izhar, Kenaniya da’ya’yansa maza su aka sa a ayyukan da ba na haikali ba, su suka zama manya da kuma alƙalai a bisa Isra’ila.
30 Asubias, issu d'Hébron, et ses frères, hommes forts, au nombre de dix- sept cents, avaient la surveillance d'Israël, sur la rive occidentale du Jourdain, pour tout ce qui concernait le service du Seigneur et le gouvernement du roi.
Daga zuriyar Hebron, Hashabiya da danginsa, su jarumawa dubu ɗaya da ɗari bakwai ne, su suke lura da Isra’ila yamma da Urdun don dukan aikin Ubangiji da kuma hidimar sarki.
31 Urie était le chef de la postérité d'Hébron, par familles paternelles; or, la quarantième année du règne de David, elle fut recensée en Jazer-Galaad, et Urie fut reconnu vaillant.
Game da zuriyar Hebron kuwa, Yeriya ne babba bisa ga tarihin zuriyar iyalansu. A shekara ta arba’in ta sarautar Dawuda, sai aka yi binciken tarihi, aka tarar jarumawa cikin zuriyar Hebron suna zama a Yazer cikin Gileyad ne.
32 Ses frères, les chefs de famille, au nombre de deux mille sept cents, étaient aussi des hommes forts; le roi les institua intendants de Ruben, de Gad et de la demi-tribu de Manassé, pour tout ce qui concernait les commandements du Seigneur et les ordres du roi.
Yeriya yana da’yan’uwa guda dubu biyu da ɗari bakwai, jarumawa da kuma kawunan iyalai, sai Sarki Dawuda ya sa su lura da mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse game da kome da ya shafi Allah da kuma al’amuran sarki.

< 1 Chroniques 26 >