< 2 Chroniques 1 >

1 Et Salomon, fils de David, s'affermit sur son trône; le Seigneur Dieu était avec lui, et il l'éleva au comble des grandeurs.
Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
2 Et Salomon parla à tout Israël, aux commandants de mille hommes, aux centeniers, aux juges, à tous les princes d'Israël et aux princes de sa famille.
Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
3 Et il alla avec toute l'Église au lieu haut de Gabaon, où était le tabernacle du témoignage de Dieu, que Moïse serviteur de Dieu avait fait dans le désert.
Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
4 Quant à l'arche de Dieu, David l'avait retirée de Cariathiarim, parce qu'il lui avait préparé et dressé un tabernacle à Jérusalem.
Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
5 Mais l'autel d'airain qu'avait fait Béséléel, fils d'Urias, fils de Hur, était à Gabaon devant le tabernacle du Seigneur, et c'est là que Salomon avec toute l'Église alla interroger Dieu.
Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
6 Et Salomon sacrifia sur l'autel d'airain devant le tabernacle du Seigneur; il y offrit un holocauste de mille victimes.
Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
7 En cette nuit-là, le Seigneur apparut à Salomon, et il lui dit: Demande ce que tu veux que je te donne.
A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
8 Et Salomon dit à Dieu: Vous avez usé d'une grande miséricorde envers David, mon père, et vous m'avez fait roi à sa place.
Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
9 Et maintenant, Seigneur Dieu, que votre nom soit engagé en faveur de David, mon père. Car, vous m'avez proclamé roi d'un peuple aussi nombreux que la poussière des champs.
To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
10 Donnez-moi la sagesse et l'intelligence, pour que je puisse bien agir devant ce peuple; car, qui jugera votre grand peuple?
Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
11 Et Dieu dit à Salomon: En récompense de ce que cela était en ton cœur, et que tu ne m'as demandé ni richesses, ni gloire, ni la mort de tes ennemis, ni de longs jours, mais que tu m'as demandé la sagesse et l'intelligence, afin de juger mon peuple sur qui je t'ai établi roi,
Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
12 Je te donne la sagesse et l'intelligence, et je te donnerai la richesse et la gloire, tellement que ton pareil n'a pas existé parmi les rois qui t'ont devancé, et n'existera pas parmi ceux qui te succèderont.
saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
13 Et Salomon s'en alla du haut lieu de Gabaon où était le tabernacle du témoignage, pour retourner à Jérusalem, et il régna sur Israël.
Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
14 Ensuite, Salomon rassembla ses chars et ses cavaliers; il eut quatorze cents chars et douze mille cavaliers; il laissa les chars dans les villes, mais la troupe demeura avec le roi à Jérusalem.
Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
15 Et le roi rendit à Jérusalem l'argent et l'or aussi communs que les pierres, et les cèdres en Judée aussi nombreux que les mûriers dans les champs.
Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
16 Salomon tirait des chevaux de l'Égypte; des marchands partaient par ses ordres, ayant été chargés de les lui acheter,
Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
17 Et ils revenaient, et ils ramenaient de l'Égypte: un char moyennant six cents sicles d'argent; un cheval moyennant cent cinquante sicles. Et il en était de même pour ce qu'ils achetaient des rois des Hettéens ou de la Syrie.
Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.

< 2 Chroniques 1 >