< Psalms 74 >

1 A contemplation by Asaph. God, why have you rejected us forever? Why does your anger smoulder against the sheep of your pasture?
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Remember your congregation, which you purchased of old, which you have redeemed to be the tribe of your inheritance: Mount Zion, in which you have lived.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Lift up your feet to the perpetual ruins, all the evil that the enemy has done in the sanctuary.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 Your adversaries have roared in the middle of your assembly. They have set up their standards as signs.
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 They behaved like men wielding axes, cutting through a thicket of trees.
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 Now they break all its carved work down with hatchet and hammers.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 They have burnt your sanctuary to the ground. They have profaned the dwelling place of your Name.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 They said in their heart, “We will crush them completely.” They have burnt up all the places in the land where God was worshipped.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 We see no miraculous signs. There is no longer any prophet, neither is there amongst us anyone who knows how long.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 How long, God, shall the adversary reproach? Shall the enemy blaspheme your name forever?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 Why do you draw back your hand, even your right hand? Take it from your chest and consume them!
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 Yet God is my King of old, working salvation throughout the earth.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 You divided the sea by your strength. You broke the heads of the sea monsters in the waters.
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 You broke the heads of Leviathan in pieces. You gave him as food to people and desert creatures.
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 You opened up spring and stream. You dried up mighty rivers.
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 The day is yours, the night is also yours. You have prepared the light and the sun.
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 You have set all the boundaries of the earth. You have made summer and winter.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Remember this, that the enemy has mocked you, LORD. Foolish people have blasphemed your name.
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 Don’t deliver the soul of your dove to wild beasts. Don’t forget the life of your poor forever.
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 Honour your covenant, for haunts of violence fill the dark places of the earth.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 Don’t let the oppressed return ashamed. Let the poor and needy praise your name.
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 Arise, God! Plead your own cause. Remember how the foolish man mocks you all day.
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 Don’t forget the voice of your adversaries. The tumult of those who rise up against you ascends continually.
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.

< Psalms 74 >