< Psalms 73 >

1 A Psalm by Asaph. Surely God is good to Israel, to those who are pure in heart.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 But as for me, my feet were almost gone. My steps had nearly slipped.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 For I was envious of the arrogant, when I saw the prosperity of the wicked.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 For there are no struggles in their death, but their strength is firm.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 They are free from burdens of men, neither are they plagued like other men.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Therefore pride is like a chain around their neck. Violence covers them like a garment.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Their eyes bulge with fat. Their minds pass the limits of conceit.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 They scoff and speak with malice. In arrogance, they threaten oppression.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 They have set their mouth in the heavens. Their tongue walks through the earth.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Therefore their people return to them, and they drink up waters of abundance.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 They say, “How does God know? Is there knowledge in the Most High?”
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Behold, these are the wicked. Being always at ease, they increase in riches.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 Surely I have cleansed my heart in vain, and washed my hands in innocence,
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 For all day long I have been plagued, and punished every morning.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If I had said, “I will speak thus”, behold, I would have betrayed the generation of your children.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 When I tried to understand this, it was too painful for me—
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 until I entered God’s sanctuary, and considered their latter end.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Surely you set them in slippery places. You throw them down to destruction.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 How they are suddenly destroyed! They are completely swept away with terrors.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 As a dream when one wakes up, so, Lord, when you awake, you will despise their fantasies.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 For my soul was grieved. I was embittered in my heart.
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 I was so senseless and ignorant. I was a brute beast before you.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Nevertheless, I am continually with you. You have held my right hand.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 You will guide me with your counsel, and afterward receive me to glory.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Whom do I have in heaven? There is no one on earth whom I desire besides you.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 My flesh and my heart fails, but God is the strength of my heart and my portion forever.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 For, behold, those who are far from you shall perish. You have destroyed all those who are unfaithful to you.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 But it is good for me to come close to God. I have made the Lord GOD my refuge, that I may tell of all your works.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< Psalms 73 >