< Mark 4 >

1 Again he began to teach by the seaside. A great multitude was gathered to him, so that he entered into a boat in the sea and sat down. All the multitude were on the land by the sea.
Ya kuma fara koyarwa a bakin teku. Akwai babban taro kewaye da shi, sai ya shiga cikin jirgin ruwa a cikin tekun, ya kuwa zauna. Duk taron kuwa na kan tudu a bakin tekun.
2 He taught them many things in parables, and told them in his teaching,
Ya koya masu abubuwa da yawa da misalai, a cikin koyawarsa ya ce masu,
3 “Listen! Behold, the farmer went out to sow.
“ku saurara! wani mai shuka ya tafi shuka.
4 As he sowed, some seed fell by the road, and the birds came and devoured it.
Yana cikin yafa iri, sai wadansu iri suka fadi a kan hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su.
5 Others fell on the rocky ground, where it had little soil, and immediately it sprang up, because it had no depth of soil.
Wadansu kuma suka fadi a kan dutse inda ba kasa dayawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin kasa.
6 When the sun had risen, it was scorched; and because it had no root, it withered away.
Da rana fa ta daga, sai suka yankwane da yake ba su da saiwa sosai, sai suka bushe.
7 Others fell amongst the thorns, and the thorns grew up and choked it, and it yielded no fruit.
Wadansu kuma suka fadi cikin kayayuwa su ka yi girma sai kayayuwan suka shake su, ba su yi tsaba ba.
8 Others fell into the good ground and yielded fruit, growing up and increasing. Some produced thirty times, some sixty times, and some one hundred times as much.”
Wadansu kuma suka fadi a kasa mai kyau, suka yi yabanya, suka yi tsaba, suka yi girma, wadansu ribi talattin wadansu sittin, wadansu kuma dari”.
9 He said, “Whoever has ears to hear, let him hear.”
Sai ya ce, Duk mai kunnen ji, ya ji,”
10 When he was alone, those who were around him with the twelve asked him about the parables.
Sa'adda Yesu yake shi kadai, wadanda suke kusa dashi tare da sha biyun suka tambaye shi ma'anar misalan.
11 He said to them, “To you is given the mystery of God’s Kingdom, but to those who are outside, all things are done in parables,
Sai ya ce masu, “ku an yardar maku, ku san asirin mulkin Allah, amma ga wadanda ba su cikinku, komai sai a cikin Misalai,
12 that ‘seeing they may see and not perceive, and hearing they may hear and not understand, lest perhaps they should turn again, and their sins should be forgiven them.’”
don gani da ido sun gani, amma ba su gane ba. ji kuma, sun ji, amma ba su fahimta ba, don kada su juyo a gafarta masu,”
13 He said to them, “Don’t you understand this parable? How will you understand all of the parables?
Ya ce masu, “Ashe, ba ku fahimci wannan misalin ba? yaushe za ku fahimci sauran?
14 The farmer sows the word.
Mai shukan nan fa maganar Allah yake shukawa.
15 The ones by the road are the ones where the word is sown; and when they have heard, immediately Satan comes and takes away the word which has been sown in them.
Wadanda suka fadi a hanyar kuwa, su ne kwatancin wadanda. a aka shuka mganar a zuciyarsu, Da suka ji, nan da nan sai shaidan ya zo ya dauke Maganar da aka shuka a zuciyarsu.
16 These in the same way are those who are sown on the rocky places, who, when they have heard the word, immediately receive it with joy.
Haka kuma wadanda aka shuka a wuri mai duwatsu, sune wadanda da zarar sun ji Maganar sai su karba da farin ciki.
17 They have no root in themselves, but are short-lived. When oppression or persecution arises because of the word, immediately they stumble.
Su kuwa basu da tushe, ba su da karfi, idan kunci ko tsanani ya zo saboda kalmar, nan da nan sai su yi tuntube.
18 Others are those who are sown amongst the thorns. These are those who have heard the word,
Wadansu kuma su ne kwatacin wadanda suka fadi cikin kayayuwa, sune wadanda suka ji Maganar,
19 and the cares of this age, and the deceitfulness of riches, and the lusts of other things entering in choke the word, and it becomes unfruitful. (aiōn g165)
amma abubuwan duniya, da rudin dukiya da kuma kwadayin wadansu abubuwa, sukan shiga su shake Maganar, har ta zama marar amfani. (aiōn g165)
20 Those which were sown on the good ground are those who hear the word, accept it, and bear fruit, some thirty times, some sixty times, and some one hundred times.”
Wadanda aka shuka a kasa mai kyau kuwa, sune kwatancin wadanda suke jin Maganar, su karba, su kuma yin amfani da ita wadansu ribi talatin, wadansu sittin, wadansu dari.”
21 He said to them, “Is a lamp brought to be put under a basket or under a bed? Isn’t it put on a stand?
ya ce masu, “Shin, ana kawo fitila a cikin gida don a rufe ta da kwando ko a ajiye ta a karkashin gado? ku kan kawo ta ne don ku dora ta a kan madorinta.
22 For there is nothing hidden except that it should be made known, neither was anything made secret but that it should come to light.
Ba abin da yake boye, da baza a sani ba ko kuma ba abinda ke asirce da bazaya bayyana a fili ba.
23 If any man has ears to hear, let him hear.”
Bari mai kunnen ji, ya ji!''
24 He said to them, “Take heed what you hear. With whatever measure you measure, it will be measured to you; and more will be given to you who hear.
Sai ya ce masu, ku mai da hankali a kan abin da kuka ji, Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a kara maka.
25 For whoever has, to him more will be given; and he who doesn’t have, even that which he has will be taken away from him.”
Domin mai abu akan karawa, marar abu kuma za a karba daga wurinsa a kuma karawa mai shi.”
26 He said, “God’s Kingdom is as if a man should cast seed on the earth,
Sai ya ce, “Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a kasa.
27 and should sleep and rise night and day, and the seed should spring up and grow, though he doesn’t know how.
A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma bai kuwa san ta yaya aka yi ba.
28 For the earth bears fruit by itself: first the blade, then the ear, then the full grain in the ear.
Kasa da kanta, takan ba da amfani, tsiro shine ne na farko,
29 But when the fruit is ripe, immediately he puts in the sickle, because the harvest has come.”
Sai kai, sa'anan sai kwaya mai kwari. Sa, adda amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi kenan.”
30 He said, “How will we liken God’s Kingdom? Or with what parable will we illustrate it?
Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta Mulki Allah? ko kuwa da wane misali za mu misalta shi?
31 It’s like a grain of mustard seed, which, when it is sown in the earth, though it is less than all the seeds that are on the earth,
Kamar kwayar zarra yake wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi kankanta cikin kwayoyi a duniya.
32 yet when it is sown, grows up and becomes greater than all the herbs, and puts out great branches, so that the birds of the sky can lodge under its shadow.”
Duk da haka in an shuka ta, sai ta yi girma fiye da duk sauran ita-tuwan da ke a jeji tayi manyan rassa, har tsuntsaye su iya yin sheka arassanta.”
33 With many such parables he spoke the word to them, as they were able to hear it.
Da misalai da yawa, irin wadannan ya yi masu Magana, dadai gwargwadon ganewarsu,
34 Without a parable he didn’t speak to them; but privately to his own disciples he explained everything.
ba ya fada masu kome sai da misali, amma a kebe, yakan bayyana wa almajiransa dukan abu.
35 On that day, when evening had come, he said to them, “Let’s go over to the other side.”
A ranan nan da yama ta yi yace masu “Mu haye wancan ketaren.”
36 Leaving the multitude, they took him with them, even as he was, in the boat. Other small boats were also with him.
Sai suka bar taron, suka tafi tare da shi acikin cikin jirgin. wadansu jirage kuma na tare da shi.
37 A big wind storm arose, and the waves beat into the boat, so much that the boat was already filled.
Sai babban hadari da iska mai karfi ya taso, rakuman ruwa kuma na ta girgizawa cikin jirgin, har jirgin ya cika.
38 He himself was in the stern, asleep on the cushion; and they woke him up and asked him, “Rabbi, don’t you care that we are dying?”
Yesu kuwa na daga karshen bayan jirgin a kan kujera, yana barci, sai suka tashe shi, suka ce masa “Malam za mu hallaka ba ka kula ba?”
39 He awoke and rebuked the wind, and said to the sea, “Peace! Be still!” The wind ceased and there was a great calm.
Sai ya farka, ya tsawata wa Iskar. Ya kuma ce wa ruwan tekun, “Ka natsu! ka yi shiru!” Sai Iskar ta kwanta, wurin duk ya yi shiru.
40 He said to them, “Why are you so afraid? How is it that you have no faith?”
Ya ce masu, “Don me kuka firgita haka? Har yanzu baku da bangaskiya ne?”
41 They were greatly afraid and said to one another, “Who then is this, that even the wind and the sea obey him?”
Sai suka tsorata kwarai suka ce wa juna, “wanene wannan kuma, wanda har Iska da teku ma suke yi masa biyayya?”

< Mark 4 >