< Leviticus 23 >

1 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak to the children of Israel, and say to them, Concerning the feasts of the LORD, which ye shall proclaim to be holy convocations, even these are my feasts.
“Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga ƙayyadaddun bukukkuwa, ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji, da za ku sanar wa mutane su riƙa kiyayewa, su zama lokutan tarurruka masu tsarki.
3 Six days shall work be done: but the seventh day is the sabbath of rest, an holy convocation; ye shall do no work in it: it is the sabbath of the LORD in all your dwellings.
“‘Akwai kwanaki shida da za ku iya yin aiki, amma rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, rana mai tsarki ga jama’a. Kada ku yi wani aiki a ko’ina kuke da zama, Asabbaci ne ga Ubangiji.
4 These are the feasts of the LORD, holy convocations, which ye shall proclaim in their seasons.
“‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa da tsarkakakkun taron jama’a za su yi a ƙayyadaddun lokuta.
5 In the fourteenth day of the first month at evening is the LORD’S passover.
Bikin Ƙetarewar Ubangiji, zai fara da yamma a ranar goma sha huɗu na wata na fari.
6 And on the fifteenth day of the same month is the feast of unleavened bread to the LORD: seven days ye must eat unleavened bread.
A rana ta goma sha biyar na wannan wata, za a fara Bikin Burodi Marar Yisti na Ubangiji. Za ku yi kwana bakwai kuna cin burodi marar yisti.
7 In the first day ye shall have an holy convocation: ye shall do no servile work in it.
A rana ta fari, ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba.
8 But ye shall offer an offering made by fire to the LORD seven days: in the seventh day is an holy convocation: ye shall do no servile work in it.
Kwana bakwai za ku miƙa hadaya ga Ubangiji da wuta. A rana ta bakwai ɗin ku yi taro mai tsarki, ba za ku kuwa yi aiki na kullum ba.’”
9 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
10 Speak to the children of Israel, and say to them, When ye shall have come into the land which I give to you, and shall reap its harvest, then ye shall bring a sheaf of the firstfruits of your harvest to the priest:
“Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, kuka kuma girbe amfanin gonarta, sai ku kawo wa firist damin hatsi na farko da kuka girbe.
11 And he shall wave the sheaf before the LORD, to be accepted for you: on the next day after the sabbath the priest shall wave it.
Zai kaɗa damin a gaban Ubangiji domin yă zama yardajje a madadinku; firist ɗin zai kaɗa shi a kashegarin Asabbaci.
12 And ye shall offer that day when ye wave the sheaf a male lamb without blemish of the first year for a burnt offering to the LORD.
A ranar da kuka kaɗa damin, dole ku miƙa hadaya ta ƙonawa na ɗan rago bana ɗaya, marar lahani ga Ubangiji,
13 And its meat offering shall be two tenth parts of fine flour mixed with oil, an offering made by fire to the LORD for a sweet savour: and its drink offering shall be of wine, the fourth part of an hin.
tare da hadaya ta gari mai laushi, humushi biyu haɗe da mai, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, mai daɗin ƙanshi, da kuma abin sha kwalaba ɗaya na ruwan inabi.
14 And ye shall eat neither bread, nor roasted grain, nor new growth, until the same day that ye have brought an offering to your God: it shall be a statute for ever throughout your generations in all your dwellings.
Ba za ku ci wani burodi, ko gasasshen hatsi, ko sabon hatsi ba, sai ran nan da kuka kawo wannan hadaya ga Allahnku. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a duk inda kuke zama.
15 And ye shall count to you from the next day after the sabbath, from the day that ye brought the sheaf of the wave offering; seven sabbaths shall be complete:
“‘Daga kashegarin Asabbaci, ranar da kuka kawo dami don hadaya ta kaɗawa, ku ƙirga cikakku makoni bakwai.
16 Even to the next day after the seventh sabbath shall ye number fifty days; and ye shall offer a new meat offering to the LORD.
Ku ƙirga kwana hamsin har zuwa kashegarin Asabbaci na bakwai, sa’an nan ku miƙa hadaya ta sabon hatsi ga Ubangiji.
17 Ye shall bring out of your habitations two wave loaves of two tenth parts: they shall be of fine flour; they shall be baked with leaven; they are the firstfruits to the LORD.
Daga ko’ina kuke da zama, ku kawo dunƙule biyu na humushin gari mai laushi da aka tuya da yisti, a matsayin hadaya ta kaɗawa ta’ya’yan fari na itatuwa ga Ubangiji.
18 And ye shall offer with the bread seven lambs without blemish of the first year, and one young bull, and two rams: they shall be for a burnt offering to the LORD, with their meat offering, and their drink offerings, even an offering made by fire, of a sweet savour to the LORD.
Tare da wannan, ku miƙa’yan raguna bakwai, kowanne bana ɗaya-ɗaya marar lahani, bijimi da kuma raguna biyu. Za su zama hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, tare da hadayunsu na hatsi, da hadayunsu na sha, hadaya da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
19 Then ye shall sacrifice one kid of the goats for a sin offering, and two lambs of the first year for a sacrifice of peace offerings.
Sa’an nan ku miƙa bunsuru ɗaya na hadaya don zunubi, da’yan raguna biyu, kowanne bana ɗaya-ɗaya, don hadaya ta salama.
20 And the priest shall wave them with the bread of the firstfruits for a wave offering before the LORD, with the two lambs: they shall be holy to the LORD for the priest.
Firist zai kaɗa’yan raguna biyun a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, tare da burodin sababbin’ya’yan fari na itatuwan. Tsarkaken hadaya ce ga Ubangiji ga firist.
21 And ye shall proclaim on the same day, that it may be an holy convocation to you: ye shall do no servile work in it: it shall be a statute for ever in all your dwellings throughout your generations.
A wannan rana za ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
22 And when ye reap the harvest of your land, thou shalt not make clean riddance of the corners of thy field when thou reapest, neither shalt thou gather any gleaning of thy harvest: thou shalt leave them to the poor, and to the stranger: I am the LORD your God.
“‘Sa’ad da kuka yi girbin gonarku, kada ku girbe har ƙarshen gefen gonar, ko ku yi kalar girbinku. Ku bar su wa matalauta da baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
23 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
24 Speak to the children of Israel, saying, In the seventh month, in the first day of the month, shall ye have a sabbath, a memorial of blowing of trumpets, an holy convocation.
“Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar farko ga wata na bakwai, za tă zama ranar hutu, rana ce ta tuni da yin taro mai tsarki na sujada da za a fara busar ƙaho.
25 Ye shall do no servile work in it: but ye shall offer an offering made by fire to the LORD.
Kada ku yi aiki na kullum, amma ku miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.’”
26 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
27 Also on the tenth day of this seventh month there shall be a day of atonement: it shall be an holy convocation to you; and ye shall afflict your souls, and offer an offering made by fire to the LORD.
“Rana ta goma ta wata bakwai, za tă zama Ranar Kafara. Sai ku yi taro mai tsarki don ku yi mūsun kanku ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.
28 And ye shall do no work in that same day: for it is a day of atonement, to make an atonement for you before the LORD your God.
Kada ku yi aiki a ranar, gama Ranar Kafara ce, sa’ad da za a yi kafara saboda ku a gaban Ubangiji Allahnku.
29 For whatever soul it may be that shall not be afflicted in that same day, he shall be cut off from among his people.
Duk wanda bai yi mūsun kansa a wannan rana ba, dole a raba shi daga mutanensa.
30 And whatever soul it may be that doeth any work in that same day, the same soul will I destroy from among his people.
Zan hallaka duk wani da ya yi aiki a wannan rana daga mutanensa.
31 Ye shall do no manner of work: it shall be a statute for ever throughout your generations in all your dwellings.
Sam ba za ku yi wani aiki ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce, wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
32 It shall be to you a sabbath of rest, and ye shall afflict your souls: in the ninth day of the month at evening, from evening to evening, shall ye celebrate your sabbath.
Asabbaci ne na hutu dominku, kuma dole ku yi mūsun kanku. Daga yamman rana ta tara ga wata, har zuwa yamma na biye, za ku kiyaye Asabbacinku.”
33 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
34 Speak to the children of Israel, saying, The fifteenth day of this seventh month shall be the feast of tabernacles for seven days to the LORD.
“Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar goma sha biyar ga wata na bakwai, za a fara Bikin Tabanakul na Ubangiji, zai kuma ɗauki kwana bakwai.
35 On the first day shall be an holy convocation: ye shall do no servile work in it.
A ranar farko za tă zama ta taro mai tsarki, kada ku yi aiki na kullum.
36 Seven days ye shall offer an offering made by fire to the LORD: on the eighth day shall be an holy convocation to you; and ye shall offer an offering made by fire to the LORD: it is a solemn assembly; and ye shall do no servile work in it.
Kwana bakwai za ku miƙa hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, a rana ta takwas, ku yi taro mai tsarki, ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji. Wannan ranar rufewar taro ce; kada ku yi aiki na kullum.
37 These are the feasts of the LORD, which ye shall proclaim to be holy convocations, to offer an offering made by fire to the LORD, a burnt offering, and a meat offering, a sacrifice, and drink offerings, every thing upon its day:
(“‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa, waɗanda za ku yi a matsayin tsarkakakkun taro, don kawo hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, hadayu na ƙonawa da hadayu na hatsi, sadaka da kuma hadayu na sha, da ake bukata kowace rana.
38 Beside the sabbaths of the LORD, and beside your gifts, and beside all your vows, and beside all your freewill offerings, which ye give to the LORD.
Waɗannan hadayu, ƙari ne a kan waɗannan na Asabbatan Ubangiji, haɗe kuma da kyautanku, da kome da kuka yi alkawari, da kuma hadayu yardar ran da za ku ba wa Ubangiji.)
39 Also in the fifteenth day of the seventh month, when ye have gathered in the fruit of the land, ye shall keep a feast to the LORD seven days: on the first day shall be a sabbath, and on the eighth day shall be a sabbath.
“‘Saboda haka, farawa daga ranar goma sha biyar ga watan bakwai, bayan kun tara hatsin gona, ku yi bikin Ubangiji kwana bakwai; rana ta fari, rana hutu ce, rana ta takwas kuma rana hutu ce.
40 And ye shall take you on the first day the boughs of goodly trees, branches of palm trees, and the boughs of thick trees, and willows of the brook; and ye shall rejoice before the LORD your God seven days.
A rana ta fari, za ku ɗebi zaɓaɓɓun’ya’yan itatuwa daga itatuwa, da rassan dabino, rassa masu ganye, da kuma ganyayen itacen wardi na rafi, ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, kwana bakwai.
41 And ye shall keep it a feast to the LORD seven days in the year. It shall be a statute for ever in your generations: ye shall celebrate it in the seventh month.
Za ku kiyaye bikin nan har kwana bakwai a kowace shekara ga Ubangiji. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsarraraki masu zuwa, ku kiyaye ta a wata na bakwai.
42 Ye shall dwell in booths seven days; all that are Israelites born shall dwell in booths:
Ku zauna a bukkoki kwana bakwai. Dukan’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa, za su zauna a bukkoki
43 That your generations may know that I made the children of Israel to dwell in booths, when I brought them out of the land of Egypt: I am the LORD your God.
don zuriyarku tă san cewa na sa Isra’ilawa suka zauna a bukkoki sa’ad da na fitar da su daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
44 And Moses declared to the children of Israel the feasts of the LORD.
Saboda haka Musa ya sanar wa Isra’ilawa ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji.

< Leviticus 23 >