< Leviticus 22 >

1 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak to Aaron and to his sons, that they separate themselves from the holy things of the children of Israel, and that they profane not my holy name in those things which they hallow to me: I am the LORD.
“Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
3 Say to them, Whoever he may be of all your seed among your generations, that approacheth the holy things, which the children of Israel hallow to the LORD, having his uncleanness upon him, that soul shall be cut off from my presence: I am the LORD.
“Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
4 Whatever man of the seed of Aaron is a leper, or hath a running issue; he shall not eat of the holy things, until he is clean. And whoever toucheth any thing that is unclean by the dead, or a man whose seed goeth from him;
“‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
5 Or whoever toucheth any creeping thing, by which he may be made unclean, or a man of whom he may take uncleanness, whatever uncleanness he hath;
da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
6 The soul who hath touched any such shall be unclean until evening, and shall not eat of the holy things, unless he shall wash his flesh with water.
duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
7 And when the sun is set, he shall be clean, and shall afterward eat of the holy things; because it is his food.
Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
8 That which dieth of itself, or is torn by beasts, he shall not eat to defile himself with it: I am the LORD.
Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
9 They shall therefore keep my ordinance, lest they bear sin for it, and die therefore, if they profane it: I the LORD sanctifieth them.
“‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
10 There shall no stranger eat of the holy thing: a sojourner of the priest, or an hired servant, shall not eat of the holy thing.
“‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
11 But if the priest shall buy any person with his money, he shall eat of it, and he that is born in his house: they shall eat of his food.
Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
12 If the priest’s daughter also shall be married to a stranger, she may not eat of an offering of the holy things.
In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
13 But if the priest’s daughter shall be a widow, or divorced, and shall have no child, and have returned to her father’s house, as in her youth, she shall eat of her father’s food: but there shall no stranger eat of it.
Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
14 And if a man shall eat of the holy thing unknowingly, then he shall put to it the fifth part, and shall give it to the priest with the holy thing.
“‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
15 And they shall not profane the holy things of the children of Israel, which they offer to the LORD;
Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
16 Or allow them to bear the iniquity of trespass, when they eat their holy things: for I the LORD sanctifieth them.
ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
17 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Speak to Aaron, and to his sons, and to all the children of Israel, and say to them, Whoever of the house of Israel, or of the strangers in Israel, that will offer his oblation for all his vows, and for all his freewill offerings, which they will offer to the LORD for a burnt offering;
“Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
19 Ye shall offer at your own will a male without blemish, of the cattle, of the sheep, or of the goats.
dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
20 But whatever hath a blemish, that shall ye not offer: for it shall not be acceptable for you.
Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
21 And whoever offereth a sacrifice of peace offerings to the LORD to accomplish his vow, or a freewill offering in cattle or sheep, it shall be perfect to be accepted; there shall be in it no blemish.
Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
22 Blind, or broken, or maimed, or having a running sore, or eczema, or scabs, ye shall not offer these to the LORD, nor make an offering by fire of them upon the altar to the LORD.
Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
23 Either a bull or a lamb that hath any thing superfluous or lacking in his parts, that mayest thou offer for a freewill offering; but for a vow it shall not be accepted.
Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
24 Ye shall not offer to the LORD that which is bruised, or crushed, or broken, or cut; neither shall ye make any offering of it in your land.
Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
25 Neither from a stranger’s hand shall ye offer the bread of your God of any of these; because their corruption is in them, and blemishes are in them: they shall not be accepted for you.
Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
26 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
27 When a bull, or a sheep, or a goat, is brought forth, then it shall be seven days under the dam; and from the eighth day on it shall be accepted for an offering made by fire to the LORD.
“Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
28 And whether it is cow or ewe, ye shall not kill it and her young both in one day.
Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
29 And when ye will offer a sacrifice of thanksgiving to the LORD, offer it at your own will.
“Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
30 On the same day it shall be eaten up; ye shall leave none of it until the next morning: I am the LORD.
Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
31 Therefore shall ye keep my commandments, and do them: I am the LORD.
“Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
32 Neither shall ye profane my holy name; but I will be hallowed among the children of Israel: I am the LORD who doth hallow you,
Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
33 That brought you out of the land of Egypt, to be your God: I am the LORD.
da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”

< Leviticus 22 >