< Jeremiah 48 >

1 Against Moab thus saith the LORD of hosts, the God of Israel; Woe to Nebo! for it is laid waste: Kiriathaim is confounded and taken: Misgab is confounded and dismayed.
Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
2 There shall be no more praise of Moab: in Heshbon they have devised evil against it; come, and let us cut it off from being a nation. Also thou shalt be cut down, O Madmen; the sword shall pursue thee.
Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
3 A voice of crying shall be from Horonaim, violence and great destruction.
Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
4 Moab is destroyed; her little ones have caused a cry to be heard.
Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
5 For in the ascent of Luhith continual weeping shall go up; for in the descent of Horonaim the enemies have heard a cry of destruction.
Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
6 Flee, save your lives, and be like the naked tree in the wilderness.
Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
7 For because thou hast trusted in thy works and in thy treasures, thou also shalt be taken: and Chemosh shall go forth into captivity with his priests and his princes together.
Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
8 And the spoiler shall come upon every city, and no city shall escape: the valley also shall perish, and the plain shall be destroyed, as the LORD hath spoken.
Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
9 Give wings to Moab, that it may flee and get away: for its cities shall be desolate, without any to dwell in them.
Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
10 Cursed be he that doeth the work of the LORD deceitfully, and cursed be he that keepeth back his sword from blood.
“La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
11 Moab hath been at ease from his youth, and he hath settled on his lees, and hath not been emptied from vessel to vessel, neither hath he gone into captivity: therefore his taste remained in him, and his scent is not changed.
“Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
12 Therefore, behold, the days come, saith the LORD, that I will send to him wanderers, that shall cause him to wander, and shall empty his vessels, and break their bottles.
Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
13 And Moab shall be ashamed of Chemosh, as the house of Israel was ashamed of Bethel their confidence.
Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
14 How say ye, We are mighty and strong men for the war?
“Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
15 Moab is laid waste, and gone up out of her cities, and his chosen young men are gone down to the slaughter, saith the King, whose name is the LORD of hosts.
Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
16 The calamity of Moab is near to come, and his affliction hasteth fast.
“Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
17 All ye that are about him, bemoan him; and all ye that know his name, say, How is the strong staff broken, and the beautiful rod!
Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
18 Thou daughter that dost inhabit Dibon, come down from thy glory, and sit in thirst; for the spoiler of Moab shall come upon thee, and he shall destroy thy strong holds.
“Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
19 O inhabitant of Aroer, stand by the way, and watch; ask him that fleeth, and her that escapeth, and say, What is done?
Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
20 Moab is confounded; for it is broken down: wail and cry; tell ye it in Arnon, that Moab is laid waste,
An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
21 And judgment is come upon the plain country; upon Holon, and upon Jahazah, and upon Mephaath,
Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
22 And upon Dibon, and upon Nebo, and upon Bethdiblathaim,
zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
23 And upon Kiriathaim, and upon Bethgamul, and upon Bethmeon,
zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
24 And upon Kerioth, and upon Bozrah, and upon all the cities of the land of Moab, far or near.
zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
25 The horn of Moab is cut off, and his arm is broken, saith the LORD.
An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
26 Make ye him drunk: for he magnified himself against the LORD: Moab also shall wallow in his vomit, and he also shall be in derision.
“Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
27 For was not Israel a derision to thee? was he found among thieves? for since thou hast spoken of him, thou didst leap for joy.
Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
28 O ye that dwell in Moab, leave the cities, and dwell in the rock, and be like the dove that maketh her nest in the sides of the hole’s mouth.
Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
29 We have heard the pride of Moab, (he is exceeding proud ) his loftiness, and his arrogance, and his pride, and the haughtiness of his heart.
“Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
30 I know his wrath, saith the LORD; but it shall not be so; his lies shall not so effect it.
Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
31 Therefore will I wail for Moab, and I will cry out for all Moab; my heart shall mourn for the men of Kirheres.
Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
32 O vine of Sibmah, I will weep for thee with the weeping of Jazer: thy plants have gone over the sea, they reach even to the sea of Jazer: the spoiler hath fallen upon thy summer fruits and upon thy vintage.
Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
33 And joy and gladness is taken from the plentiful field, and from the land of Moab; and I have caused wine to fail from the winepresses: none shall tread with shouting; their shouting shall be no shouting.
Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
34 From the cry of Heshbon even to Elealeh, and even to Jahaz, have they uttered their voice, from Zoar even to Horonaim, as an heifer of three years old: for the waters also of Nimrim shall be desolate.
“Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
35 Moreover I will cause to cease in Moab, saith the LORD, him that offereth in the high places, and him that burneth incense to his gods.
A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
36 Therefore my heart shall sound for Moab like pipes, and my heart shall sound like pipes for the men of Kirheres: because the riches that he hath gotten have perished.
“Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
37 For every head shall be bald, and every beard clipped: upon all the hands shall be cuttings, and upon the loins sackcloth.
An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
38 There shall be lamentation generally upon all the housetops of Moab, and in its streets: for I have broken Moab like a vessel in which is no pleasure, saith the LORD.
A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
39 They shall wail, saying, How is it broken down! how hath Moab turned the back with shame! so shall Moab be a derision and a dismaying to all them about him.
“Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
40 For thus saith the LORD; Behold, he shall fly as an eagle, and shall spread his wings over Moab.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
41 Kerioth is taken, and the strong holds are surprised, and the mighty men’s hearts in Moab at that day shall be as the heart of a woman in her pangs.
Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
42 And Moab shall be destroyed from being a people, because he hath magnified himself against the LORD.
Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
43 Fear, and the pit, and the snare, shall be upon thee, O inhabitant of Moab, saith the LORD.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
44 He that fleeth from the fear shall fall into the pit; and he that getteth out of the pit shall be taken in the snare: for I will bring upon it, even upon Moab, the year of their punishment, saith the LORD.
“Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
45 They that fled stood under the shadow of Heshbon because of the force: but a fire shall come out of Heshbon, and a flame from the midst of Sihon, and shall devour the corner of Moab, and the crown of the head of the tumultuous ones.
“A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
46 Woe be to thee, O Moab! the people of Chemosh perisheth: for thy sons are taken captives, and thy daughters captives.
Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
47 Yet will I bring again the captivity of Moab in the latter days, saith the LORD. Thus far is the judgment of Moab.
“Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.

< Jeremiah 48 >