< Deuteronomy 26 >

1 And it shall be, when thou hast come in to the land which the LORD thy God giveth thee for an inheritance, and dost possess it, and dwellest in it;
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
2 That thou shalt take of the first of all the fruit of the earth, which thou shalt bring of thy land that the LORD thy God giveth thee, and shalt put it in a basket, and shalt go to the place which the LORD thy God shall choose to place his name there.
sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
3 And thou shalt go to the priest that shall be in those days, and say to him, I profess this day to the LORD thy God, that I have come to the country which the LORD swore to our fathers to give us.
ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
4 And the priest shall take the basket from thy hand, and set it down before the altar of the LORD thy God.
Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
5 And thou shalt speak and say before the LORD thy God, A Syrian ready to perish was my father, and he went down to Egypt, and sojourned there with a few, and became there a nation, great, mighty, and populous:
Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
6 And the Egyptians oppressed us, and afflicted us, and laid upon us hard bondage:
Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
7 And when we cried to the LORD God of our fathers, the LORD heard our voice, and looked on our affliction, and our labour, and our oppression:
Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
8 And the LORD brought us out of Egypt with a mighty hand, and with an outstretched arm, and with great terribleness, and with signs, and with wonders:
Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
9 And he hath brought us into this place, and hath given us this land, even a land that floweth with milk and honey.
Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
10 And now, behold, I have brought the firstfruits of the land, which thou, O LORD, hast given me. And thou shalt set it before the LORD thy God, and worship before the LORD thy God:
yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
11 And thou shalt rejoice in every good thing which the LORD thy God hath given to thee, and to thy house, thou, and the Levite, and the stranger that is among you.
Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
12 When thou hast finished tithing all the tithes of thy increase the third year, which is the year of tithing, and hast given it to the Levite, the stranger, the fatherless, and the widow, that they may eat within thy gates, and be filled;
Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
13 Then thou shalt say before the LORD thy God, I have brought away the hallowed things out of my house, and also have given them to the Levite, and to the stranger, to the fatherless, and to the widow, according to all thy commandments which thou hast commanded me: I have not transgressed thy commandments, neither have I forgotten them:
Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
14 I have not eaten of it in my mourning, neither have I taken away any of it for any unclean use, nor given any of it for the dead: but I have hearkened to the voice of the LORD my God, and have done according to all that thou hast commanded me.
Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
15 Look down from thy holy habitation, from heaven, and bless thy people Israel, and the land which thou hast given us, as thou didst swear to our fathers, a land that floweth with milk and honey.
Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
16 This day the LORD thy God hath commanded thee to perform these statutes and judgments: thou shalt therefore keep and do them with all thy heart, and with all thy soul.
Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
17 Thou hast proclaimed the LORD this day to be thy God, and to walk in his ways, and to keep his statutes, and his commandments, and his judgments, and to hearken to his voice:
Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
18 And the LORD hath proclaimed thee this day to be his special people, as he hath promised thee, and that thou shouldest keep all his commandments;
Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
19 And to make thee high above all nations which he hath made, in praise, and in name, and in honour; and that thou mayest be an holy people to the LORD thy God, as he hath spoken.
Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.

< Deuteronomy 26 >