< Deuteronomy 25 >

1 If there shall be a controversy between men, and they come to judgment, that the judges may judge them; then they shall justify the righteous, and condemn the wicked.
Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
2 And it shall be, if the wicked man be worthy to be beaten, that the judge shall cause him to lie down, and to be beaten before his face, according to his fault, by a certain number.
in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
3 Forty stripes he may give him, and not exceed: lest, if he should exceed, and beat him above these with many stripes, then thy brother should seem vile to thee.
amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
4 Thou shalt not muzzle the ox when he treadeth out the grain.
Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
5 If brethren shall dwell together, and one of them shall die, and have no child, the wife of the dead shall not marry outside the family to a stranger: her husband’s brother shall go in to her, and take her to him for a wife, and perform the duty of an husband’s brother to her.
In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
6 And it shall be, that the firstborn which she beareth shall succeed in the name of his brother who is dead, that his name may not be blotted out from Israel.
Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
7 And if the man shall not desire to take his brother’s wife, then let his brother’s wife go up to the gate to the elders, and say, My husband’s brother refuseth to raise up to his brother a name in Israel, he will not perform the duty of my husband’s brother.
Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
8 Then the elders of his city shall call him, and speak to him: and if he shall stand to it, and say, I desire not to take her;
Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
9 Then shall his brother’s wife come to him in the presence of the elders, and loose his shoe from off his foot, and spit in his face, and shall answer and say, So shall it be done to that man that will not build up his brother’s house.
sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
10 And his name shall be called in Israel, The house of him that hath his shoe loosed.
Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
11 When men strive together one with another, and the wife of the one draweth near to deliver her husband from the hand of him that smiteth him, and putteth forth her hand, and taketh him by the secrets:
In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
12 Then thou shalt cut off her hand, thy eye shall not pity her.
sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
13 Thou shalt not have in thy bag differing weights, a great and a small.
Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
14 Thou shalt not have in thy house differing measures, a great and a small.
Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
15 But thou shalt have a perfect and just weight, a perfect and just measure shalt thou have: that thy days may be lengthened in the land which the LORD thy God giveth thee.
Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
16 For all that do such things, and all that do unrighteously, are an abomination to the LORD thy God.
Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
17 Remember what Amalek did to thee by the way, when ye had come forth from Egypt;
Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
18 How he met thee by the way, and smote those behind thee, even all that were feeble behind thee, when thou wast faint and weary; and he feared not God.
Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
19 Therefore it shall be, when the LORD thy God hath given thee rest from all thy enemies on all sides, in the land which the LORD thy God giveth thee for an inheritance to possess it, that thou shalt blot out the remembrance of Amalek from under heaven; thou shalt not forget it.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!

< Deuteronomy 25 >