< Exodus 6 >

1 Then Yahweh said to Moses, “Now you will see what I will do to Pharaoh. You will see this, for he will let them go because of my strong hand. Because of my strong hand, he will drive them out of his land.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu za ka gan abin da zan yi da Fir’auna. Zan sa shi dole yă bar su su tafi, har ma yă iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”
2 God spoke to Moses and said to him, “I am Yahweh.
Allah ya kuma ce wa Musa, “Ni ne Ubangiji.
3 I appeared to Abraham, to Isaac, and to Jacob as God Almighty; but by my name, Yahweh, I was not known to them.
Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku da kuma ga Yaƙub a matsayin Allah Maɗaukaki, amma sunan nan nawa Ubangiji, ban bayyana kaina a gare su ba.
4 I also established my covenant with them, in order to give them the land of Canaan, the land where they lived as non-citizens, the land in which they wandered about.
Na kuma kafa alkawari da su don in ba su ƙasar Kan’ana, inda suka yi zaman baƙunci.
5 Moreover, I have heard the groaning of the Israelites whom the Egyptians have enslaved, and I have called to mind my covenant.
Ban da haka ma, na ji nishe-nishen Isra’ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuma tuna da alkawarina.
6 Therefore, say to the Israelites, 'I am Yahweh. I will bring you out from slavery under the Egyptians, and I will free you from their power. I will rescue you with a display of my power, and with mighty acts of judgment.
“Saboda haka, ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ni ne Ubangiji, zan kuma fitar da ku daga bauta ta Masarawa. Zan’yantar da ku daga zama bayinsu, da ƙarfina zan fanshe ku, in kawo hukunci mai zafi a kansu, don in cece ku.
7 I will take you to myself as my people, and I will be your God. You will know that I am Yahweh your God, who brought you out from slavery under the Egyptians.
Zan ɗauke ku tamƙar mutanena, in kuma zama Allahnku. Sa’an nan za ku sani Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga wahalar Masarawa.
8 I will bring you into the land that I swore to give to Abraham, to Isaac, and to Jacob. I will give it to you as a possession. I am Yahweh.'”
Zan kuwa kawo ku a ƙasar da na rantse da hannun da na ɗaga sama, cewa zan ba wa Ibrahim, wa Ishaku, da kuma wa Yaƙub. Zan ba da ita gare ku gādo. Ni ne Ubangiji.’”
9 When Moses told this to the Israelites, they would not listen to him because of their discouragement about their harsh slavery.
Musa ya faɗa wa Isra’ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne a gare shi ba, don ɓacin rai saboda tsananin aikin bauta.
10 Then Yahweh spoke to Moses, saying,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
11 “Go tell Pharaoh, king of Egypt, to let the people of Israel go from his land.”
“Koma ka ce wa Fir’auna sarkin Masar, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.”
12 Moses said to Yahweh, “If the Israelites have not listened to me, why will Pharaoh listen to me, since I am not good at speaking?”
Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “In Isra’ilawa ba su ji ni ba, yaya Fir’auna zai ji ni, da yake ina magana da ƙyar?”
13 Yahweh spoke to Moses and to Aaron. He gave them a command for the Israelites and for Pharaoh, king of Egypt, to bring the Israelites out of the land of Egypt.
Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna game da Isra’ilawa da Fir’auna sarkin Masar, ya umarce su su fitar da Isra’ilawa daga Masar.
14 These were the heads of their fathers' houses: The sons of Reuben, the firstborn of Israel, were Hanok, Pallu, Hezron, and Karmi. These were the clan ancestors of Reuben.
Waɗannan su ne shugabannin iyalansu.’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila su ne, Hanok da Fallu, Hezron da Karmi. Waɗannan su ne dangin Ruben.
15 The sons of Simeon were Jemuel, Jamin, Ohad, Jakin, Zohar, and Shaul—the son of a Canaanite woman. These were the clan ancestors of Simeon.
’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana. Waɗannan su ne dangin Simeyon.
16 Here are listed the names of the sons of Levi, together with their descendants. They were Gershon, Kohath, and Merari. Levi lived until he was 137 years old.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Lawi maza bisa ga abin da aka rubuta, Gershon, Kohat da Merari. Lawi ya yi shekara 137.
17 The sons of Gershon were Libni and Shimei.
’Ya’yan Gershon maza, bisa ga dangi su ne, Libni da Shimeyi.
18 The sons of Kohath were Amram, Izhar, Hebron, and Uzziel. Kohath lived until he was 133 years old.
’Ya’yan Kohat maza, su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel. Kohat ya yi shekara 133.
19 The sons of Merari were Mahli and Mushi. These became the clan ancestors of the Levites, together with their descendants.
’Ya’yan Merari maza, su ne, Mali da Mushi. Waɗannan su ne dangin Lawi bisa ga abin da aka rubuta.
20 Amram married Jochebed, his father's sister. She bore him Aaron and Moses. Amram lived 137 years and then died.
Amram ya auri’yar’uwar mahaifinsa Yokebed, wadda ta haifa masa Haruna da Musa. Amram ya yi shekara 137.
21 The sons of Izhar were Korah, Nepheg, and Zichri.
’Ya’yan Izhar maza, su ne, Kora, Nefeg da Zikri.
22 The sons of Uzziel were Mishael, Elzaphan, and Sithri.
’Ya’yan Uzziyel maza, su ne, Mishayel, Elzafan da Sitri.
23 Aaron married Elisheba, daughter of Amminadab, sister of Nahshon. She bore him Nadab and Abihu, Eleazar and Ithamar.
Haruna ya auri Elisheba,’yar Amminadab,’yar’uwar Nashon, sai ta haifa masa Nadab da Abihu, Eleyazar da Itamar.
24 The sons of Korah were Assir, Elkanah, and Abiasaph. These were the clan ancestors of the Korahites.
’Ya’yan Kora maza, su ne, Assir, Elkana da Abiyasaf. Waɗannan su ne dangin Kora.
25 Eleazar, Aaron's son, married one of the daughters of Putiel. She bore him Phinehas. These were the heads of the fathers' houses among the Levites, together with their descendants.
Eleyazar ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin’yan matan Futiyel, sai ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan Lawi, dangi, dangi.
26 These two men were the Aaron and Moses to whom Yahweh said, “Bring out the Israelites from the land of Egypt, by their groups of fighting men.”
Wannan Haruna da Musa ne, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana ya ce, “Ku fitar da Isra’ilawa daga Masar ɓangare-ɓangare.”
27 Aaron and Moses spoke to Pharaoh, king of Egypt, to allow them bring out the Israelites from Egypt. These were the same Moses and Aaron.
Su ne suka yi magana da Fir’auna sarkin Masar game da fitar da Isra’ilawa daga Masar, wannan Musa da Haruna.
28 When Yahweh spoke to Moses in the land of Egypt,
Ana nan, sa’ad da Ubangiji ya yi magana da Musa a Masar,
29 he said to him, “I am Yahweh. Say to Pharaoh, king of Egypt, everything that I will tell you.”
ya ce masa, “Ni ne Ubangiji. Sai ka faɗa wa Fir’auna sarkin Masar kome da na faɗa maka.”
30 But Moses said to Yahweh, “I am not good at speaking, so why will Pharaoh listen to me?”
Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, ina magana da ƙyar, ƙaƙa Fir’auna zai kasa kunne gare ni?”

< Exodus 6 >