< Exodus 5 >

1 After these things happened, Moses and Aaron went to Pharaoh and said, “This is what Yahweh, the God of Israel, says: 'Let my people go, so they can have a festival for me in the wilderness.'”
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 Pharaoh said, “Who is Yahweh? Why should I listen to his voice and let Israel go? I do not know Yahweh; moreover, I will not let Israel go.”
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 They said, “The God of the Hebrews has met with us. Let us go on a three-day journey into the wilderness and sacrifice to Yahweh our God so that he does not attack us with plague or with the sword.”
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 But the king of Egypt said to them, “Moses and Aaron, why are you taking the people from their work? Go back to your work.”
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 He also said, “There are now many people in our land, and you are making them stop their work.”
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
6 On that same day, Pharaoh gave a command to the people's taskmasters and foremen. He said,
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 “Unlike before, you must no longer give the people straw to make bricks. Let them go and gather straw for themselves.
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 However, you must still demand from them the same number of bricks as they made before. Do not accept any fewer, because they are lazy. That is why they are calling out and saying, 'Allow us to go and sacrifice to our God.'
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 Increase the workload for the men so that they keep at it and pay no more attention to deceptive words.”
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 So the people's taskmasters and foremen went out and informed the people. They said, “This is what Pharaoh says: 'I will no longer give you any straw.
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 You yourselves must go and get straw wherever you can find it, but your workload will not be reduced.'”
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
12 So the people scattered throughout all the land of Egypt to gather stubble for straw.
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 The taskmasters kept urging them and saying, “Finish your work, just as when straw was given to you.”
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 Pharaoh's taskmasters beat the Israelite foremen, those same men whom they had put in charge of the workers. The taskmasters kept asking them, “Why have you not produced all the bricks required of you, either yesterday and today, as you used to do in the past?”
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 So the Israelite foremen came to Pharaoh and cried out to him. They said, “Why are you treating your servants this way?
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 No straw is being given to your servants anymore, but they are still telling us, 'Make bricks!' We, your servants, are even beaten now, but it is the fault of your own people.”
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 But Pharaoh said, “You are lazy! You are lazy! You say, 'Allow us to go sacrifice to Yahweh.'
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 So now go back to work. No more straw will be given to you, but you must still make the same number of bricks.”
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 The Israelite foremen saw that they were in trouble when they were told, “You must not reduce the daily number of bricks.”
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 They met Moses and Aaron, who were standing outside the palace, as they went away from Pharaoh.
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 They said to Moses and Aaron, “May Yahweh look at you and punish you, because you have made us offensive in the sight of Pharaoh and his servants. You have put a sword in their hand to kill us.”
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 Moses went back to Yahweh and said, “Lord, why have you caused trouble for this people? Why did you send me in the first place?
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 Ever since I came to Pharaoh to speak to him in your name, he has caused trouble for this people, and you have not set your people free at all.”
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”

< Exodus 5 >