< Luke 16 >

1 And he sayd also vnto his disciples. Ther was a certayne rych man which had a stewarde that was acused vnto him that he had wasted his goodes.
Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
2 And he called him and sayd vnto him: How is it that I heare this of the? Geve a comptes of thy steward shippe: For thou mayste be no longer stewarde.
Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
3 The stewarde sayd wt in him selfe: what shall I do? for my master will take awaye fro me ye stewarde shippe. I canot digge and to begge I am ashamed.
“Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
4 I woote what to do yt when I am put out of ye stewardshippe they maye receave me into their houses.
Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
5 Then called he all his masters detters and sayd vnto ye fyrst: how moche owest thou vnto my master?
“Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
6 And he sayd: an hondred tonnes of oyle. And he sayd to him: take thy bill and syt doune quickly and wryte fiftie.
“Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
7 Then sayd he to another: what owest thou? And he sayde: an hondred quarters of wheate. He sayd to him: Take thy bill and write foure scoore.
“Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
8 And the lorde comended the vniust stewarde because he had done wysly. For ye chyldren of this worlde are in their kynde wyser then ye chyldren of lyght. (aiōn g165)
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
9 And I saye also vnto you: make you frendes of the wicked mammon that when ye shall departe they may receave you into everlastinge habitacions. (aiōnios g166)
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
10 He that is faithfull in that which is leste ye same is faithfull in moche. And he yt is vnfaithfull in ye least: is vnfaithfull also in moche.
“Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
11 So then yf ye have not ben faithfull in ye wicked mamon? who will beleve you in that which is true?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
12 And yf ye have not bene faithfull in another manes busines: who shall geve you youre awne?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
13 No servaunt can serve. ii. masters for other he shall hate ye one and love ye other or els he shall lene to the one and despyse the other. Ye can not serve God and mammon.
“Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
14 All these thinges herde the pharises also which were coveteous and they mocked him.
Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
15 And he sayd vnto the: Ye are they which iustifie youre selves before me: but God knoweth youre hertes. For ye which is highlie estemed amoge me is abhominable in yt sight of god
Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
16 The lawe and the Prophetes raygned vntyll the tyme of Iohn: and sence that tyme the kyngdom of God is preached and every man stryveth to goo in.
“An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
17 Soner shall heven and erth perisshe then one tytle of the lawe shall perisshe.
Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
18 Whosoever forsaketh his wyfe and marieth another breaketh matrimony. And every man which marieth her that is devorsed from her husbande committeth advoutry also.
“Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
19 Ther was a certayne ryche man which was clothed in purple and fyne bysse and fared deliciously every daye.
“An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
20 And ther was a certayne begger named Lazarus whiche laye at his gate full of soores
A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
21 desyringe to be refresshed with the cromes whiche fell from the ryche manes borde. Neverthelesse the dogges came and licked his soores.
Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
22 And yt fortuned that the begger dyed and was caried by the angelles into Abrahas bosome. The riche man also died and was buried.
“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
23 And beinge in hell in tormetes he lyfte vp his eyes and sawe Abraham a farre of and Lazarus in his bosome (Hadēs g86)
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
24 and he cryed and sayd: father Abraham have mercy on me and sende Lazarus that he maye dippe the tippe of his fynger in water and cole my tonge: for I am tourmented in this flame.
Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
25 But Abraha sayd vnto him Sonne remembre that thou in thy lyfe tyme receavedst thy pleasure and contrary wyse Lazarus payne. Now therfore is he comforted and thou art punysshed.
“Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 Beyonde all this bitwene you and vs ther is a greate space set so that they which wolde goo from thence to you cannot: nether maye come from thence to vs.
Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
27 Then he sayd: I praye the therfore father send him to my fathers housse.
“Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
28 For I have fyve brethren: for to warne the left they also come into this place of tourmet.
gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
29 Abraha sayd vnto him: they have Moses and the Prophetes let them heare them.
“Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
30 And he sayd: naye father Abraham but yf one came vnto the from the ded they wolde repent.
“Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
31 He sayd vnto him: If they heare not Moses and ye prophetes nether will they beleve though one roose from deeth agayne.
“Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”

< Luke 16 >