< Luke 22 >

1 The feaste of swete breed drue nye whiche is called ester
Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
2 and the hye prestes and Scribes sought how to kyll him but they feared the people.
manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
3 Then entred Satan into Iudas whose syr name was Iscariot (which was of the nombre of the twelve)
Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
4 and he went his waye and comuned with the hye Prestes and officers how he might betraye him to them.
Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
5 And they were glad: and promysed to geve him money.
Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
6 And he consented and sought oportunite to betraye him vnto them when the people were awaye.
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
7 Then came ye daye of swete breed when of necessite the esterlambe must be offered.
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
8 And he sent Peter and Iohn sayinge: Goo and prepare vs the ester lambe that we maye eate.
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
9 They sayde to him. Where wilt thou yt we prepare?
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
10 And he sayd vnto them. Beholde when ye be entred into the cite ther shall a man mete you bearinge a pitcher of water him folowe into the same housse yt he entreth in
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
11 and saye vnto ye good ma of ye housse. The master sayeth vnto ye: where is ye gest chamber where I shall eate myne ester lambe wt my disciples?
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
12 And he shall shew you a greate parloure paved. Ther make redy.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
13 And they wet and foude as he had sayd vnto the: and made redy ye ester lambe.
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
14 And when the houre was come he sate doune and the twelve Apostles with him.
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
15 And he sayde vnto them: I have inwardly desyred to eate this ester lambe with you before yt I suffre.
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
16 For I saye vnto you: hence forthe I will not eate of it eny moore vntill it be fulfilled in the kingdome of God.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
17 And he toke the cup and gave thankes and sayde. Take this and devyde it amonge you.
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
18 For I saye vnto you: I will not drinke of the frute of the vyne vntill the kingdome of God be come.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
19 And he toke breed gave thankes and gave to them sayinge: This is my body which is geven for you. This do in the remembraunce of me.
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
20 Lykewyse also when they had supped he toke the cup sayinge: This cup is the newe testament in my bloud which shall for you be shedde.
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
21 Yet beholde the honde of him that betrayeth me is with me on the table.
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
22 And ye sonne of man goeth as it is appoynted: But wo be to yt man by whom he is betrayed.
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
23 And they began to enquyre amoge them selves which of them it shuld be that shuld do that.
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
24 And ther was a stryfe amoge the which of them shuld be taken for the greatest.
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
25 And he sayde vnto them: the kynges of the getyls raygne over them and they that beare rule over them are called gracious lordes.
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
26 But ye shall not be so. But he that is greatest amonge you shalbe as the yongest: and he that is chefe shalbe as the minister.
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
27 For whether is greater he that sitteth at meate: or he that serveth? Is not he that sitteth at meate? And I am amoge you as he that ministreth.
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
28 Ye are they which have bidden with me in my temptacions.
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
29 And I apoynt vnto you a kyngdome as my father hath appoynted to me:
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
30 that ye maye eate and drynke at my table in my kyngdome and sit on seates and iudge the twelve tribes of Israell.
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
31 And the Lorde sayde: Simon Simon beholde Satan hath desired you to sifte you as it were wheate:
“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
32 bnt I have prayed for the that thy faith fayle not. And when thou arte converted strengthe thy brethre.
Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
33 And he sayd vnto him. Lorde I am redy to go with the in to preson and to deth.
Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
34 And he sayde: I tell the Peter the cocke shall not crowe this daye tyll thou have thryse denyed yt thou knewest me.
Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 And he sayde vnto them: when I sent you with out wallet and scripe and shoes? lacked ye eny thinge? And they sayd no.
Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
36 And he sayde to them: but nowe he that hath a wallet let him take it vp and lykewyse his scrippe. And he that hath no swearde let him sell his coote and bye one.
Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
37 For I saye vnto you that yet that which is written must be performed in me: even with the wycked was he nombred. For those thinges which are written of me have an ende.
A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
38 And they sayde: Lorde beholde here are two sweardes. And he sayde vnto them: it is ynough.
Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
39 And he came out and went as he was wote to mounte olivete. And the disciples folowed him.
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
40 And when he came to the place he sayde to the: praye lest ye fall into temptacio.
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
41 And he gate him selfe from them about a stones cast and kneled doune and prayed
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
42 sayinge: Father yf thou wilt withdrawe this cup fro me. Neverthelesse not my will but thyne be be fulfilled.
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
43 And ther appered an angell vnto him from heaven confortinge him.
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
44 And he was in an agonye and prayed somwhat longer. And hys sweate was lyke droppes of bloud tricklynge doune to the grounde.
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
45 And he rose vp from prayer and came to his disciples and foude them slepinge for sorowe
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
46 and sayde vnto them: Why slepe ye? Ryse and praye lest ye fall into temptacion.
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
47 Whill he yet spake: beholde ther came a company and he that was called Iudas one of the twelve wet before them and preased nye vnto Iesus to kysse him.
Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
48 And Iesus sayd vnto him: Iudas betrayest thou ye sonne of man with a kysse?
Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
49 When they which were about him sawe what wolde folow they sayde vnto him. Lorde shall we smite with swearde.
Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
50 And one of them smote a servaut of ye hiest preste of all and smote of his right eare.
Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
51 And Iesus answered and sayd: Soffre ye thus farre forthe. And he touched his eare and healed him.
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
52 Then Iesus sayde vnto the hye prestes and rulers of the temple and the elders which were come to him. Be ye come out as vnto a thefe with sweardes and staves?
Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
53 When I was dayly with you in the teple ye stretched not forth hondes agaynst me. But this is even youre very houre and the power of darcknes.
Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
54 Then toke they him and ledde him and brought him to the hye prestes housse. And peter folowed a farre of.
Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
55 When they had kyndled a fyre in the middes of the palys and were set doune to geder Peter also sate doune amonge them.
Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
56 And wone of the wenches behelde him as he sate by the fyer and set good eyesight on him and sayde: this same was also with him.
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 Then he denyed hym sayinge: woman I knowe him not
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
58 And after a lytell whyle another sawe him and sayde: thou arte also of them. And Peter sayd man I am not.
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
59 And aboute the space of an houre after another affirmed sayinge: verely even this felowe was with hym for he is of Galile
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
60 and Peter sayde: ma I woote not what thou sayest. And immediatly whyll he yet spake the cocke crewe.
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
61 And the Lorde tourned backe and loked apon Peter. And Peter remembred the wordes of the Lorde how he sayde vnto him before ye cocke crowe thou shalt denye me thryse.
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
62 And Peter went out and wepte bitterly.
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
63 And the men that stode about Iesus mocked him and smoote him
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
64 and blyndfolded him and smoote his face. And axed him sayinge: arede who it is that smoote ye?
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
65 And many other thinges despytfullye sayd they agaynst him.
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
66 And assone as it was daye the elders of the people and the hye prestes and scribes came to gedder and ledde him into their counsell sayinge:
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
67 arte thou very Christ? tell vs. And he sayde vnto the: yf I shall tell you ye will not beleve
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
68 And yf also I axe you ye will not answere me or let me goo.
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
69 Herafter shall the sonne of man sit on the ryght honde of the power of God.
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
70 Then sayde they all: Arte thou then the sonne of God? He sayd to them: ye saye yt I am.
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
71 Then sayde they: what nede we eny further witnes? We oure selves have herde of his awne mouthe.
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”

< Luke 22 >