< Hebrews 8 >

1 The main point of [all] that [I] have written is that we have a Supreme Priest like that. He has sat down to rule [MTY] with God [EUP] at the place of greatest honor in heaven.
Abin da muke magana a nan shi ne, muna da irin wannan babban firist, wanda ya zauna a hannun dama na kursiyin Maɗaukaki a sama,
2 He ministers in the Most Holy Place, that is, in the true place [of worship in heaven]. That is a place that [Moses’] tent [represented]. The Lord set up the true place of worship. No human [set it up].
wanda yake hidima a cikin wuri mai tsarki, tabanakul na gaskiya wanda Ubangiji ne ya kafa, ba mutum ba.
3 Every Supreme Priest was appointed {[God] appointed every Supreme Priest} to offer [to God] gifts and sacrifices [for people who sinned]. So, since [Christ became a Supreme Priest], he also had to offer something.
Da yake dole kowane babban firist da aka naɗa yă miƙa baye-baye da hadayu, haka ma wannan ya bukaci yă kasance da abin da zai miƙa.
4 Since there are already [Jewish] priests who offer gifts as God’s laws [require], if Christ were [now living] on the earth, he would not be a Supreme Priest.
Da a ce yana a duniya ne, da bai zama firist ba, domin a nan akwai mutanen da doka ta naɗa don su miƙa baye-baye.
5 The [Jewish] priests perform rituals which are only a model [DOU] of [what Christ would do in heaven] [MTY]. What [God] told Moses when Moses was about to set up the tent [for worshipping him supports the idea that those rituals were only a model. God said], “Be sure that you [(sg)] make everything according to the model that I showed you on [Sinai] Mountain!”
Suna hidima a cikin tsattsarkan wuri wanda yake hoto da kuma siffar abin da yake cikin sama. Shi ya sa aka gargaɗi Musa sa’ad da yana dab da gina tabanakul cewa, “Ka lura fa, ka yi kome daidai bisa ga zānen da aka nuna maka a kan dutsen.”
6 But now as it is, [Christ] ministers in a more excellent way [than the Jewish priests do]. Likewise, the [new] covenant that he established [between God and people] is better [than the old one. When the new covenant was established] {[God established the new covenant]}, he promised us better things [than the laws that God gave Moses did].
Amma hidimar da Yesu ya karɓa tana da fifiko a kan tasu, kamar yadda alkawarin da shi ne yake matsakanci ya fi na dā fifiko nesa, an kuma kafa shi a kan alkawura mafi kyau.
7 If that first covenant had been perfectly adequate [LIT], God would not have thought that he needed another [covenant/agreement to replace it]. But [it was not adequate, so he needed a new one].
Gama da a ce alkawari na fari ba shi da wani laifi, da ba sai an sāke neman wani ba.
8 Because God declared [that the Israelites] were guilty [of not obeying the first covenant, he wanted a new covenant. This is what] ([a prophet/Jeremiah]) [wrote about that]: The Lord says, “Listen! There will soon be a time when I will make a new covenant with the people [MTY] of Israel and the people [MTY] of Judah.
Amma Allah ya sami mutane da laifi ya ce, “Ina gaya muku lokaci yana zuwa, sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
9 That covenant will not be like the covenant that I made with their ancestors when I led them out of Egypt [MET] [like a father leads a child] by the hand. They did not continue to [obey] my covenant, so I rejected them,” says the Lord.
Ba zai zama kamar irin alkawarin da na yi da kakanni-kakanninsu sa’ad da na kama hannunsu don in fitar da su daga Masar ba, domin ba su yi aminci da alkawarina ba, sai na juya musu baya, in ji Ubangiji.
10 “This is the covenant that I will make with the Israelites [MTY], after [the first covenant has ended] [MTY],” says the Lord: “I will enable them to understand my laws [MTY], and I will enable them to obey them (OR, truly know them) [MTY] sincerely. I will be their God, and they will be my people [DOU].
Wannan shi ne alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila, bayan lokacin nan, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu. Zan zama Allahnsu, su kuwa za su zama mutanena.
11 [As a result], no one will [need to] teach a fellow citizen or tell his fellow kinsmen, ‘[You need to] know the Lord,’ because all [my people] will know me: [My people] of every status [will know me].
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa ba, balle mutum yă ce wa ɗan’uwansa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin dukansu za su san ni, daga ƙaraminsu zuwa babba.
12 I will mercifully [forgive them for] the wicked things they have done. I will no longer [consider] that [they are guilty for] [DOU] [their] sins.”
Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuma ƙara tuna da zunubansu ba.”
13 Since God spoke about a new [covenant], he considered that the first [covenant] was no longer in use, and that it would soon disappear, just like [anything that] gets old [will disappear] [MET, DOU].
Ta wurin kira wannan alkawari “sabo,” ya mai da na farin tsoho ke nan; abin da yake tsoho yana kuma daɗa tsufa, zai shuɗe nan ba da daɗewa ba.

< Hebrews 8 >