< James 1 >

1 [I], James, am a servant of God and the Lord Jesus Christ. [I am writing this letter] to [all] the Jewish people [who trust in Christ] (OR, to all God’s people) who are scattered throughout the world. [I send my] greetings to [you all].
Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
2 My fellow believers, rejoice greatly, [even] when you experience various kinds of difficulties/troubles.
Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
3 [God sometimes allows you to experience difficulties in order to] test whether or not you will continue to trust [him. Whenever that happens, you need to] realize more and more that [if you continue to trust him], you will be able to bravely/patiently endure difficulties.
domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
4 Keep on enduring difficulties [bravely/patiently by trusting God more and more firmly] [PRS], in order that you may become all that he intends you to be [DOU] (OR, [spiritually] mature and complete), not lacking (any [good quality/anything you need to conduct your lives as God wants you to]).
Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
5 If anyone of you does not know how to act wisely [in order to endure difficulties/trials well], he should ask God [to show him what he should do, because] God wholeheartedly/gladly helps all people [who ask] and does not scold [anyone for asking. Those who ask], God will give them wisdom to know [what they should do].
In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
6 But [when you] ask [God], you should firmly trust him. You should not doubt [that he wants to help you always], because people who keep doubting God are [unstable/changeable] [SIM] like a wave of the sea that is blown back and forth by the wind {that goes back and forth when the wind blows} [DOU, SIM].
Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
7 Indeed, people [who doubt] should not think that the Lord [God] will do anything [that they request him to do],
Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
8 [because they are] people who cannot decide [whether they will commit themselves to God, and they are] unstable/undecided in everything that they do.
shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
9 Believers who are poor should be happy [that God] considers them very valuable (OR, has exalted them [spiritually]) [MTY].
Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
10 And [believers] who are rich should be happy [that] they have humbled themselves [in order to trust in Jesus Christ] (OR, but rich people [can only] take pride [in the fact that God] will humble them [when he judges everyone] [IRO]), because they [and their riches] [MTY] will pass away, just like wild flowers [wither] [SIM].
Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
11 When the sun rises, the scorching hot wind dries plants, and their flowers fall and are no longer beautiful. Similarly, rich people will die [MET] while they are busy working, [leaving behind their riches].
Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
12 [God] is pleased with people who bravely/patiently endure difficulties. And when, [by bravely enduring difficulties], they have proved [that they truly trust him], he will give them [eternal] life. That is the reward [MET] that he has promised to give to those who love him.
Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
13 If people are tempted to do something that is evil, they should not think that it is God who is tempting them, because [God is totally/completely good]. He never tempts anyone [to do what is evil], nor can he ever be tempted to [do anything] evil.
Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
14 But people strongly desire to do evil [PRS] things, [and as a result] they are tempted by those desires {those desires stimulate them} to do something evil [PRS, DOU].
amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
15 Then, [because] they have desired [MET] to do evil [PRS] things, they begin to [MET] do [PRS] them. And when they have become ones who [habitually] do what is evil [MET], [if they do not turn away from their sinful behavior], they will be separated from God forever.
Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
16 My fellow believers whom I love, stop deceiving yourselves, [thinking that God does evil things].
Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
17 [The truth is that God], our heavenly Father [MTY], does only good [DOU] things [for us, in order to help us become] all that he intends us to be. He is not like all the things [in the sky] that he created to give light, [because they] change; [that is, they do not shine the same all the time]. But God never changes. [He is always good].
Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
18 [And because] he wanted [to help us], he gave us [spiritual] life as a result of our [trusting in his] true message. So now we have become the first ones of [all the people] [MET] that he created [to] ([be totally dedicated to/completely belong to]) [him].
Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
19 My fellow believers whom I love, you know (OR, I want you to now) that every one of you should be eager to pay attention to [God’s true message]. Don’t speak [without thinking], nor get angry easily,
’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
20 because when any one [of you gets] angry, you will not be doing the righteous things that God [wants] you [to do].
gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
21 So stop doing all kinds of evil [DOU] things, and humbly obey (OR, submit to) the message that [God] put in your (inner beings/hearts), [because] he is able to save you [SYN] [if you accept his message].
Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
22 Do [what God commands in] his message. Do not only listen [to it, because people who only listen to it and do not obey it] are wrong when they think [that God will save them].
Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
23 Some people hear God’s message but do not do [what it says] [MET]. They are like someone who looks at his face in a mirror [SIM].
Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
24 Although he looks at himself, he goes away [from the mirror] and immediately forgets what he looks like.
bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
25 But other people look closely at [God’s] message, which is perfect and which sets people free [to voluntarily do what God wants them to do]. And if they continue [to examine God’s message] and do not just hear it and then forget it, but do [what God tells them to do], God will bless them because of what they do.
Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
26 Some people think that they worship God in the right way, but they habitually say evil things [MTY]. Those people are wrong in thinking [SYN] [that they worship God rightly]. The fact is [that they] worship God (in vain/uselessly).
In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
27 [One of the things that God has told us to do] is to take care of orphans and widows who suffer hardship. [Those who do that and] who do not think or act immorally like those who do not obey God [MTY] truly [DOU] worship God, [who is our] Father, and God approves of them.
Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.

< James 1 >