< Mark 7 >

1 And are gathered together to Him the Pharisees and some of the scribes having come from Jerusalem.
Farisiyawa da waɗansu malaman dokoki waɗanda suka zo daga Urushalima, suka taru kewaye da Yesu.
2 And they had seen some of the disciples of Him (that *no) with defiled hands, That is unwashed, (are eating *N+kO) (the *no) bread (they found fault; *K)
Sai suka ga waɗansu daga cikin almajiransa suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta, wato, da ba a wanke ba.
3 For the Pharisees and all the Jews only unless with a fist they shall wash the hands, not eat holding the tradition of the elders;
(Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci, sai sun wanke hannuwa sarai tukuna, yadda al’adun dattawa suka ce.
4 and [on coming] from [the] market (now *o) (when may come *ko) only unless (they shall wash *NK+o) not they eat; and other things many there are which they received to keep washings of cups and vessels and utensils and couches for dining.
Sa’ad da suka dawo daga wurin kasuwanci, dole su wanke hannu kafin su ci abinci. Sukan kuma kiyaye waɗansu al’adu da yawa, kamar wanken kwafuna, tuluna da butoci.)
5 (And *N+kO) questioned Him the Pharisees and the scribes; Because of why not walk the disciples of You according to the tradition of the elders, but (with unsanctified *N+KO) hands eat the bread?
Saboda haka, Farisiyawa da malaman dokoki suka tambayi Yesu, suka ce, “Don me almajiranka ba sa bin al’adun dattawa, a maimakon haka suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta?”
6 And (answering *k) He said to them (that: *ko) Rightly prophesied Isaiah concerning you hypocrites, as it has been written (that *no) This people with the lips Me honors, but the heart of them far away is kept from Me.
Ya amsa ya ce, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci game da ku munafukai; kamar yadda yake a rubuce cewa, “‘Waɗannan mutane da baki suke girmama ni, amma zukatansu sun yi nesa da ni.
7 In vain now they worship Me teaching [as] doctrines [the] precepts of men.’
A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokokin mutane ne kawai.’
8 Having neglected (for *k) the commandment of God you hold to the tradition of men (washings of vessels and of cups and more like things many things you do. *KO)
Kun yar da umarnan Allah, kuna bin al’adun mutane.”
9 And He was saying to them; Neatly do you set aside the commandment of God that the tradition of you (you may maintain. *N+kO)
Ya kuma ce musu, “Kuna da hanya mai sauƙi na ajiye umarnan Allah a gefe ɗaya, don ku kiyaye al’adunku!
10 Moses for said; do honor the Father of you and the mother of you,’ and The [one] speaking evil of father or mother in death should end.’
Gama Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’kuma, ‘Duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.’
11 You yourselves however say [that]: if may say a man to the father or to the mother; [It is] Corban, that is a gift, whatever if from me you shall be profited,
Amma ku, kukan ce, in mutum ya ce wa mahaifinsa, ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da ya kamata ku samu daga wurina, Korban ne,’ (wato, abin da aka keɓe wa Allah),
12 (and *ko) no longer no longer you do allow him no [thing] to do for the father (of him *k) or for the mother (of him *k)
sa’an nan haka ba kwa ƙara barinsa yă yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa wani abu.
13 making void the word of God for the tradition of you which you have handed down; And like [things] such many you do.
Ta haka kuke rushe maganar Allah ta wurin al’adun da kuke miƙa wa’ya’yanku. Haka kuma kuke yin abubuwa da yawa.”
14 And having called to [Him] (again *N+KO) the crowd He was saying to them; (do listen to *N+kO) Me all and (do understand. *N+kO)
Sai Yesu ya sāke kiran taron wurinsa ya ce, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimci wannan.
15 No [thing] there is outside of the man entering into him which is able to defile him but the [things] (out of the man *NO) proceeding (from of him *k) (that *ko) are those which are defiling the man.
Ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi. Sai dai abin da ya fita daga cikin mutum ne, yake ƙazantar da shi.”
16 (if anyone has ears to hear he should hear. *KO)
17 And when He went into [the] house from the crowd, were asking Him the disciples of Him (concerning *k) (the parable. *N+kO)
Bayan ya bar taron, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
18 And He says to them; Thus also you yourselves without understanding are? Surely you understand that everything outside entering into the man not is able him to defile?
Ya ce, “Ashe, ba ku da saurin ganewa? Ba ku gane cewa ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi.
19 because not it enters of him into the heart but into the belly and into the sewer goes out, (purifying *N+kO) all the food.
Gama ba ya shiga cikin zuciyarsa, sai dai cikin tumbinsa, sa’an nan kuma yă fita daga jikinsa.” (Da faɗin haka, Yesu ya nuna tsabtar kowane irin abinci.)
20 He was saying now that That out of the man going forth, that [is what] defiles the man.
Ya ci gaba, “Abin da yake fitowa daga mutum ne yake ƙazantar da shi.
21 Within for from the heart of men thoughts evil go forth sexual immorality thefts murders,
Gama daga ciki, daga zuciyar mutane, mugayen tunani suke fitowa, fasikanci, sata, kisankai, zina,
22 adulteries covetous desires, wickednesses, deceit, sensuality, an eye evil, slander, pride, foolishness;
kwaɗayi, ƙeta, ruɗu, ƙazantaccen sha’awa, kishi, ɓata suna, girman kai da kuma wauta.
23 All these evils from within go forth and it defiles the man.
Duk waɗannan mugayen abubuwa daga cikin suke fitowa, suna kuma ƙazantar da mutum.”
24 (and *ko) From there (also *no) having risen up He went away into the (region *N+KO) of Tyre (and Sidon. *KO) And having entered into a house no [one] He was wishing to know [it] and not He was able to be hidden.
Sai Yesu ya bar wurin, ya kuma tafi wajajen Taya. Ya shiga wani gida, bai kuwa so kowa yă sani ba. Duk da haka, bai iya ɓoye kasancewarsa ba.
25 (But immediately *NO) having heard (for *k) a woman about Him of whom had the little daughter of her spirit unclean, having come she fell at the feet of Him;
Da jin labarinsa, sai wata mace wadda ƙaramar diyarta tana da mugun ruhu, ta zo ta durƙusa a gabansa.
26 Now the woman was Gentile Syrophoenician by race, and was asking Him that the demon (He may cast forth *N+kO) out of the daughter of her.
Macen kuwa mutuniyar Hellenawa ce, an haife ta a Funisiya a Suriya. Ta roƙi Yesu yă fitar da aljani da yake jikin diyarta.
27 (And *N+kO) (Jesus *k) (He was saying *N+kO) to her; do permit first to be satisfied the children; not for it is good to take the bread of the children and to the dogs to cast [it].
Yesu ya ce mata, “Da farko, bari’ya’ya su ci su ƙoshi tukuna, gama ba daidai ba ne, a ɗauki burodin yara a jefa wa karnukansu.”
28 But she answered and she says to Him; (yes *KO) Lord, even (for *k) the dogs under the table (eat *N+kO) of the crumbs of the children.
Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, ko karnuka ma da suke ƙarƙashin tebur, sukan ci burbuɗin da suke fāɗuwa daga abincin yara.”
29 And He said to her; Because of this word do go, has gone forth out of the daughter of you the demon.
Sai ya ce mata, “Saboda irin wannan amsa, ki tafi, aljanin ya rabu da diyarki.”
30 And having gone away to the home of her she found the (child *N+KO) (laid *N+kO) on (the bed *N+kO) and the demon having left.
Ta tafi gida, ta tarar da diyarta kwance a gado, aljanin kuwa ya fita.
31 And again having departed from the region of Tyre He came (through *N+KO) Sidon (to *N+kO) the Sea of Galilee through [the] midst of the region of [the] Decapolis.
Sai Yesu ya bar wajajen Taya, ya bi ta Sidon har zuwa Tekun Galili da kuma cikin yankin Dekafolis.
32 And they bring to Him a deaf man (and *no) who spoke with difficulty and they implore Him that He may lay on him the hand.
A can ne waɗansu mutane suka kawo masa wani kurma, wanda da ƙyar yake magana. Sai suka roƙe shi yă ɗibiya hannunsa a kan mutumin.
33 And having taken away him from the crowd aside privately He put the fingers of Him to the ears of him, and having spit He touched the tongue of him,
Bayan da ya jawo shi gefe, sai Yesu ya sa yatsotsinsa a kunnuwan mutumin, ya tofa miyau ya kuma taɓa harshen mutumin.
34 and having looked up to heaven He sighed deeply and He says to him; Ephphatha! that is do be opened
Ya ɗaga kai sama, ya ja numfashi mai zurfi, sa’an nan ya ce masa, “Effata!” (Wato, “Buɗe!”).
35 And (immediately *NK) (were opened *N+kO) his ears, and was loosed the band of the tongue of him, and he was speaking plainly.
Bayan ya faɗa haka, sai kunnuwan mutumin suka buɗe, harshensa kuma ya kunce, sai ya fara magana sarai.
36 And He instructed them that to no one (they may speak; *N+kO) As much as however (He himself *k) them was instructing, (they themselves *no) more excessive were proclaiming [it].
Yesu ya umarce su, kada su gaya wa kowa. Amma ƙara yawan kwaɓarsu ƙara yawan yaɗa labarin suke ta yi.
37 And above measure above measure they were astonished saying; Well all things He has done both the deaf He makes to hear and (the *NK) mute to speak.
Mutane suka cika da mamaki, suka ce, “Kai, ya yi kome daidai. Har ma yana sa kurame su ji, bebaye kuma su yi magana.”

< Mark 7 >