< Mark 6 >

1 And He went out from there and (came *N+kO) into the hometown of Him, and follow Him the disciples of Him.
Yesu ya tashi daga can ya tafi garinsa, tare da almajiransa.
2 And when was becoming [the] Sabbath He began to teach in the synagogue; and many hearing were astonished saying; From where to this [man] these things, and what [is] the wisdom which having been given (to Him *N+kO) (for *k) even (the *no) miracles such through the hands of Him (are done? *N+kO)
Da Asabbaci ya kewayo, sai ya fara koyarwa a cikin majami’a, mutane da yawa da suka saurare shi, suka yi mamaki. Suna tambaya, “Ina mutumin nan ya sami waɗannan abubuwa? Wace hikima ce wannan da aka ba shi, har da yana yin ayyukan banmamaki haka!
3 Surely this is the carpenter, the son of Mary (and *no) brother (now *k) of James and of Joses and of Judas and of Simon? And surely are the sisters of Him here with us? And they were offended by Him.
Ashe, wannan ba shi ne kafinta nan ba? Shin, ba shi ne ɗan Maryamu ba, ba shi ne ɗan’uwan su Yaƙub, Yusuf, Yahuda da kuma Siman ba? Ashe,’yan’uwansa mata kuma ba suna nan tare da mu ba?” Sai suka ji haushinsa.
4 (And *no) was saying (now *k) to them Jesus that Not is a prophet without honor only except in the hometown of him and among the relatives of him and in the household of him.
Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa kaɗai, da kuma cikin’yan’uwansa, da cikin gidansa ne, annabi ba shi da daraja.”
5 And not He was able there to do not any work of power only except on a few sick having laid the hands He healed.
Bai iya yin ayyukan banmamaki a wurin ba, sai dai ɗibiya hannuwansa da ya yi a kan mutane kima da suke da cututtuka, ya kuwa warkar da su.
6 And (He was marveling *NK+o) because of the unbelief of them. And He was going the villages around teaching.
Ya kuwa yi mamaki ƙwarai don rashin bangaskiyarsu. Sai ya Yesu zazzaga ƙauyuka yana koyarwa.
7 And He calls near the Twelve and He began them to send forth two [by] two and He was gaving to them authority over the spirits unclean
Ya kira Sha Biyun nan wurinsa, ya aike su biyu-biyu, ya kuma ba su iko bisa mugayen ruhohi.
8 And He instructed to them that nothing they may take for [the] journey only except a staff alone, no bread nor bag nor in the belt money,
Ga dai umarnansa, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, sai dai sanda ba burodi, ba jaka, ba kuɗi a ɗamararku.
9 but having put on yourselves sandals, and not (may put on *NK+o) two tunics.
Ku sa takalma, amma ban da riga fiye da waɗanda kuka sa.
10 And He was saying to them; Wherever (maybe *NK+o) you shall enter into a house, there do remain until maybe you may go out from there.
Duk sa’ad da kuka shiga wani gida, ku zauna nan sai kun bar garin.
11 And (whatever *N+kO) maybe (place *no) not (he may receive *N+kO) you nor may hear you, departing from there do shake off the dust which [is] under the feet of you for a testimony against them. (Amen I say to you more tolerable will be for Sodom or for Gomorrah in day of judgment than for the for city that [one]. *K)
In kuwa a wani wuri ba a karɓe ku, ba a kuwa saurare ku ba, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita, a matsayin shaida a kansu.”
12 And having gone out (they proclaimed *N+kO) that (they may repent, *N+kO)
Suka fita, suna yi wa’azi, suna ce wa mutane su tuba.
13 And demons many they were casting out and were anointing with oil many sick and were healing [them].
Suka fitar da aljanu da yawa, suka shafa wa marasa lafiya da yawa mai, suka kuwa warkar da su.
14 And heard King Herod; well known for became the name of Him. And (they were saying *N+kO) that John the [one] baptizing (he has been raised *N+kO) out from [the] dead and because of this operate the miraculous powers in him.
Sarki Hiridus ya ji wannan labari, gama sunan Yesu ya bazu a ko’ina. Waɗansu suna cewa, “An tashe Yohanna Mai Baftisma daga matattu ne, shi ya sa yana da ikon yin ayyukan banmamakin nan.”
15 Others (however *no) were saying that Elijah He is; Others now were saying that A prophet (is or *K) like one of the prophets.
Waɗansu suka ce, “Ai, Iliya ne.” Har wa yau waɗansu suka ce, “Ai, annabi ne, kamar ɗaya daga cikin annabawan dā.”
16 Having heard now Herod (was saying *N+kO) (that: *k) Whom I myself beheaded John — he ([it] is he himself *k) is risen (from *ko) (dead. *KO)
Amma da Hiridus ya ji haka, sai ya ce, “Ai, Yohanna ne, mutumin da na yanke masa kai, shi ne ya tashi daga matattu!”
17 Himself for Herod having sent he seized John and bound him in prison on account of Herodias the wife of Philip the brother of him because her he had married;
Gama Hiridus da kansa ya ba da umarni a kama Yohanna, ya kuma sa aka daure shi, aka sa shi a kurkuku. Ya yi haka saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus, wadda ya aura.
18 Were saying for John to Herod that Not it is lawful for you to have the wife of the brother of you.
Gama Yohanna ya yi ta ce wa Hiridus, “Ba daidai ba ne bisa ga doka, ka ɗauki matar ɗan’uwanka.”
19 And Herodias was holding it against him and he was wishing him to kill and not he was able;
Saboda haka, Hiridiyas ta ƙulla munafunci game da Yohanna, ta kuma so ta kashe shi. Amma ba tă iya ba,
20 for Herod was afraid of John knowing him [to be] a man righteous and holy and he was keeping safe him. And when having heard him much (he was perplexed *N+KO) and gladly him was hearing.
domin Hiridus yana jin tsoron Yohanna, ya kuma kāre shi sosai, da sanin cewa shi mutum ne mai adalci da kuma mai tsarki. Duk sa’ad da Hiridus ya saurari Yohanna, yakan damu ƙwarai, duk da haka, yakan so yă ji shi.
21 And when was coming [a] day opportune when Herod on the birthday of him a banquet (made *N+kO) for the great men of him and for the chief captains and for the leading [men] of Galilee
A ƙarshe, ta sami zarafi. A ranar murnar haihuwar Hiridus, ya yi biki domin hakimansa, da shugabannin sojojinsa, da kuma manyan mutanen Galili.
22 and when was entering the daughter (of him *N+KO) Herodias and when having danced (and *ko) (she pleased *N+kO) Herod and those reclining with [him] said (now *o) the king to the girl; do ask me whatever if you shall wish, and I will give to you.
Sa’ad da diyar Hiridiyas ta shigo, ta kuma yi rawa, sai ta gamshi Hiridus tare da baƙinsa. Sai Sarkin ya ce wa yarinyar, “Ki tambaye ni kome da kike so, ni kuwa zan ba ki.”
23 And he swore to her (greatly *N) whatever (thing *N+kO) if me you shall ask I will give you until half of the kingdom of mine.
Ya yi mata alkawari da rantsuwa cewa, “Duk abin da kika roƙa, zan ba ki, ko da rabin mulkina ne.”
24 (And *no) (now *k) having gone out she said to the mother of her; What (shall I ask for myself? *N+kO) And she said; The head of John the [one] (baptizing. *N+kO)
Sai ta fita ta ce wa mahaifiyarta, “Me zan roƙa?” Ta ce, “Kan Yohanna Mai Baftisma.”
25 And having entered immediately with haste to the king she asked saying; I desire that at once may you give to me on a platter the head of John the Baptist.
Nan da nan, sai yarinyar ta yi hanzari zuwa wajen sarki da roƙon, “Ina so ka ba ni kan Yohanna Mai Baftisma a cikin tasa, yanzu-yanzu nan.”
26 And encompassingly sorrowful having been made the king on account of the oaths and those (reclining with [him] *N+KO) not was he willing to refuse her.
Sai sarki ya yi baƙin ciki ƙwarai, amma saboda rantsuwar da kuma baƙinsa, bai so yă hana ta ba.
27 And immediately having sent the king an executioner he commanded (to be brought *N+kO) the head of him. (And *N+kO) having gone he beheaded him in the prison
Nan take, sai ya aiki mai aiwatar da kisa da umarni ya kawo kan Yohanna. Mutumin ya je ya yanke kan Yohanna a kurkuku.
28 and brought the head of him on a platter and gave it to the girl, and the girl gave it to the mother of her.
Ya kuma kawo kan a tasa ya ba yarinyar. Ita kuma ta ba wa mahaifiyarta.
29 And having heard [it] the disciples of him came and they took up the body of him and laid it in [a] tomb.
Da almajiran Yohanna suka sami labari, sai suka zo suka ɗauki jikinsa suka binne a kabari.
30 And are gathered together the apostles to Jesus and they related to him all things (and *k) how much they had done and how much they had taught.
Manzannin suka taru kewaye da Yesu, suka ba shi rahoton duk abin da suka yi, da kuma suka koyar.
31 And (He speaks *N+kO) to them; Come you yourselves yourselves apart [your] own to [a] solitary place and (do rest *N+kO) a little; Were for those coming and those going [are] many, and not even to eat were they able.
To, saboda mutane da yawa suna kai da kawowa, har ma ba su sami damar cin abinci ba, sai ya ce musu, “Ku zo mu kaɗaita inda ba kowa don ku ɗan huta.”
32 And they went away (in *no) the boat into [a] solitary place on [their] own.
Sai suka tafi a jirgin ruwa su kaɗai, inda ba kowa.
33 And they saw them going (crowds *K) and (recognized *NK+O) (him *k) many and on foot from all the cities ran together there and went before them (and together went to him. *K)
Amma mutane da yawa waɗanda suka ga tashinsu, sun gane su, sai suka ruga da gudu a ƙafa daga dukan birane, suka riga su kaiwa can.
34 And having gone out He saw (Jesus *k) a great crowd and was moved with compassion toward (them *N+kO) because they were like sheep not having a shepherd. And He began to teach them many things.
Da Yesu ya sauka, ya ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu, gama kamar tumaki suke waɗanda ba su da makiyayi. Sai ya fara koya musu abubuwa da yawa.
35 And already when the hour late being having come to Him the disciples of Him (were saying *N+kO) that Desolate is the place, and already [it is] an hour late;
A lokacin nan yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce masa, “Wurin nan ƙauye ne, ga shi kuma lokaci ya ƙure.
36 do dismiss them that having gone to the surrounding region and villages they may buy for themselves something (loaves for *K) may eat (not they have. *K)
Ka sallami mutanen su shiga ƙauyukan da suke kurkusa, su sayi wa kansu wani abu, su ci.”
37 But answering He said to them; do give to them you yourselves [something] to eat. And they say to Him; Having gone shall we buy denarii two hundred of bread and [then] (we will give *N+kO) them [it] to eat?
Sai ya amsa ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Suka ce masa, “Ai, wannan zai ɗauki albashin wata takwas na mutum! Mu je mu kashe yawan kuɗin nan a burodi mu ba su su ci?”
38 And He says to them; How many loaves have you do go (and *k) do see. And having known they say; Five and two fish.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Burodi nawa kuke da su? Je ku duba.” Da suka duba, sai suka ce, “Biyar da kifi biyu.”
39 And He commanded them (to recline *NK+o) all groups [by] groups on the green grass.
Sa’an nan Yesu ya umarce su su sa dukan mutanen su zazzauna ƙungiya-ƙungiya a kan ɗanyar ciyawa.
40 And they sat down groups [by] groups (by *N+kO) hundreds and (by *N+kO) fifties.
Haka suka zazzauna a ƙungiyar ɗari-ɗari, da kuma hamsin-hamsin.
41 And having taken the five loaves and the two fish, having looked up to the heaven He blessed and He broke the loaves and He was giving [them] to the disciples of Him that (they may set before *N+kO) them, And the two fish He divided among all.
Ya ɗauki burodi guda biyar da kifin nan biyu, ya ɗaga kai sama, ya yi godiya, ya kakkarya burodin. Sai ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutane. Ya kuma rarraba kifi biyun a tsakaninsu duka.
42 And ate all and were satisfied,
Kowa ya ci, ya ƙoshi,
43 And they took up (of fragments *N+kO) twelve (hand-baskets fullness *N+kO) and of the fish.
almajiran suka kwashe gutsattsarin burodin da na kifin cike da kwanduna goma sha biyu.
44 And were those having eaten of the loaves (about *K) five thousand men.
Yawan mutanen da suka ci kuwa maza dubu biyar ne.
45 And immediately He compelled the disciples of Him to climb into the boat and to go before to the other side to Bethsaida until He himself (dismisses *N+kO) the crowd.
Nan da nan Yesu ya sa almajiransa su shiga jirgin ruwa, su sha gabansa zuwa Betsaida, shi kuma yă sallami taron.
46 And having taken leave of them He departed into the mountain to pray.
Bayan ya bar su, sai ya hau kan dutse don yă yi addu’a.
47 And when evening having come was the boat in [the] midst of the sea, and He himself alone upon the land.
Da yamma ta yi, jirgin ruwan yana tsakiyar tafkin, Yesu kuma yana can a ƙasa shi kaɗai.
48 And (seeing *N+kO) them straining in the rowing, was for the wind contrary to them, (and *k) About [the] fourth watch of the night He comes to them walking on the sea and He was wishing to pass by them.
Ya ga almajiran suna fama da tuƙi saboda iska tana gāba da su. Wajen tsara ta huɗu na dare, sai ya tafi wurinsu, yana takawa a kan tafkin. Ya yi kamar zai wuce su,
49 And having seen Him on the sea walking they thought (that *no) a ghost ([it] is, *N+kO) and cried out;
amma da suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai suka yi tsammani fatalwa ce. Sai suka yi ihu,
50 All for Him saw and were troubled. (now *N+kO) immediately He spoke with them and says to them; Take courage! I myself am [He], not do fear.
domin dukansu sun gan shi, suka kuma tsorata. Nan da nan ya yi magana da su ya ce, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
51 And He went up to them into the boat, and ceased the wind. And exceedingly over excessive in themselves they were amazed (and were marveling; *K)
Sai ya shiga jirgin ruwan tare da su, iskar kuma ta kwanta. Dukansu suka yi mamaki,
52 not for they understood by the loaves, (but *N+KO) were of them the heart hardened.
gama ba su fahimci al’amarin burodin nan ba, don zuciyarsu ta taurare.
53 And having passed over to the land they came (to *no) Gennesaret and drew to shore.
Da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret, suka daure jirgin a ƙugiya.
54 And when were exiting they out of the boat immediately having recognized Him
Da fitowarsu daga jirgin, sai mutane suka gane Yesu.
55 (they ran around *N+kO) all the (region *N+kO) that (and *no) they began on the mats those sick being to carry about to wherever they were hearing that (there *ko) He is.
Suka gama yankin da gudu, suna ɗaukan marasa lafiya a kan tabarmai zuwa duk inda suka ji yake.
56 And wherever maybe He was entering into villages or (into *no) cities or (into *no) fields in the marketplaces they were laying those ailing and were begging Him that only only of the fringe the clothing of Him they shall touch, and as many as maybe (touched *N+kO) Him were being healed.
Duk inda ya shiga, cikin ƙauyuka, birane ko karkara, sai su kwantar da marasa lafiya a bakin kasuwa. Suka roƙe shi yă bari su taɓa gefen rigarsa kawai, kuma duk waɗanda suka taɓa shi kuwa, suka warke.

< Mark 6 >