< Luke 4 >

1 Jesus then full of [the] Spirit Holy returned from the Jordan and was led by the Spirit (into the wilderness *N+kO)
Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
2 days forty being tempted by the devil. And not He ate no [thing] in the days those, and when were ending they (afterward *K) He was hungry.
kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
3 (and *k) Said (then *no) to Him the devil; If [the] Son You are of God, do speak to the stone this that it may become bread.
Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
4 And answered to him Jesus (saying: *k) It has been written that Not on bread alone will live the man’ (but upon everything declaration of God. *KO)
Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
5 And having led up Him (devil into mountain high *K) he showed to Him all the kingdoms of the world in a moment of time
Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
6 And said to Him the devil; To You will I give authority this all and the glory of it, for to me myself it has been delivered and to whom (maybe *NK+o) I shall wish I give it;
Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
7 You yourself therefore if You shall worship before (me *N+kO) will be Yours (everything. *N+kO)
Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
8 And answering Jesus said to him (do go *KO) (behind me Satan; *K) It has been written: (for *k) [The] Lord the God of you you will worship and Him only you will serve.’
Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
9 (and *k) He led (also *no) Him to Jerusalem and set (him *ko) upon the pinnacle of the temple and said to Him; If (the *k) Son You are of God, do cast Yourself from here down;
Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
10 It has been written for that To the angels of Him He will give orders concerning You to guard You;
Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
11 and that in [their] hands will they bear You, otherwise otherwise You may strike against a stone the foot of You.’
kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
12 And answering He said to him Jesus that It has been said; Not you will test [the] Lord the God of you.’
Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
13 And having finished every temptation the devil departed from Him until an opportune time.
Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
14 And returned Jesus in the power of the Spirit to Galilee, and a report went out into all the surrounding region concerning Him.
Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
15 And He himself was teaching in the synagogues of them being glorified by all.
Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
16 And He came to Nazareth where He was raised, and He entered according to the being customary to Him on the day of the Sabbaths into the synagogue and stood up to read.
Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
17 And there was given to Him [the] scroll of the prophet Isaiah; and (having unrolled *NK+o) the scroll He found the place where it was written
An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
18 [The] Spirit of [the] Lord [is] upon Me myself, of which because He has anointed Me (to evangelise *N+kO) to [the] poor, He has sent Me (to heal the bruised heart *K) to proclaim to [the] captives deliverance and to [the] blind recovery of sight, to send forth [the] oppressed in deliverance,
“Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
19 to proclaim [the] year of [the] Lord’s favor.
in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
20 And having rolled up the scroll having delivered [it] to the attendant He sat down, and of all the eyes in the synagogue were fixed upon Him.
Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
21 He began then to say to them that Today has been fulfilled Scripture this in the hearing of you.
Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
22 And all were bearing witness to Him and they were marveling at the words of the grace which are proceeding out of the mouth of Him and they were saying; (surely *N+kO) [the] son is of Joseph this?
Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
23 And He said to them; Surely you will say to Me proverb this; Physician do heal yourself! As much as we have heard has been done (in *N+kO) Capernaum, do perform also here in the hometown of You.
Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
24 He said then; Amen I say to you that no prophet acceptable is in the hometown of him.
Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
25 In truth now I say to you; many widows there were in the days of Elijah in Israel when was shut up the heaven for years three and months six, when there was a famine great upon all the land;
Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
26 and to none of them was sent Elijah only except to Zarephath (of Sidon *N+kO) to a woman a widow.
Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
27 And many lepers were in Israel in the time of Elisha the prophet; and none of them was cleansed only except Naaman the Syrian.
Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
28 And were filled all with anger in the synagogue hearing these things;
Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
29 and having risen up they cast Him out of the city and led Him unto (the *k) brow of the hill upon which the town had been built of them (in order *N+kO) to throw over him.
Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
30 He himself however having passed through [the] midst of them was going away.
Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
31 And He went down to Capernaum a city of Galilee And He was teaching them on the Sabbaths.
Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
32 and they were astonished at the teaching of Him for with authority was the message of Him.
Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
33 And in the synagogue was a man having a spirit of a demon unclean, and he cried out in a voice loud;
A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
34 (saying *ko) Ha! What to us and to You, Jesus of Nazareth? Are You come to destroy us? I know You who are, the Holy [One] of God.
“Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
35 And rebuked him Jesus saying; do be silent and do come forth (out of *N+kO) him! And having thrown him the demon into the midst it came out from him in nothing having hurt him.
Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
36 And came astonishment upon all, and they were speaking to one another saying; What word [is] this for with authority and power He commands the unclean spirits, and they come out?
Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
37 And was spreading [the] report concerning Him into every place of the surrounding region.
Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
38 Having risen up then (out of *N+kO) the synagogue He entered into the house of Simon. (The *k) mother-in-law then of Simon was oppressed with a fever great, and they appealed to Him for her.
Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
39 And having stood over her He rebuked the fever, and it left her; immediately then having arisen she was serving them.
Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
40 When is setting now the sun (all *N+kO) as many as had [any] ailing with diseases various brought them to Him; and on one each of them the hands (having laid He was healing *N+kO) them.
Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
41 Were going out now also demons from many (shouting out *N+kO) and saying that You yourself are (Christ *K) the Son of God. And rebuking [them] not was He allowing them to speak because they knew the Christ Him to be.
Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
42 When was arriving now daybreak having gone out He went into a solitary place, and the crowds (were sought after *N+kO) Him and they came up to Him and were detaining Him of the not to go from them.
Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
43 But He said to them that Also to the other towns to evangelise Me it behooves of the kingdom of God, because (for *N+kO) this (have I been sent forth. *N+kO)
Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
44 And He was preaching (in the synagogues *N+kO) (of Judea. *N+KO)
Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.

< Luke 4 >