< Luke 3 >

1 In year then fifteenth of the reign of Tiberius Caesar, when is being governor Pontius Pilate of Judea and when is being tetrarch of Galilee Herod, Philip now the brother when he is being tetrarch of Ituraea and of Trachonitis [the] region and Lysanias of Abilene being tetrarch
A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
2 during ([the] high priesthood *N+kO) of Annas and Caiaphas, came [the] declaration of God upon John the of Zechariah son in the wilderness.
kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
3 And he went into all the surrounding region of the Jordan proclaiming a baptism of repentance for forgiveness of sins
Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
4 as it has been written in [the] book of [the] words of Isaiah the prophet (saying: *k) [The] voice of one crying in the wilderness do prepare the way of [the] Lord, straight do make the paths of Him.
Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
5 Every valley will be filled and every mountain and hill will be made low; and will become the crooked into (straight *NK+o) and the rough into ways smooth;
Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
6 and will behold all flesh the salvation of God.
kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
7 He was saying therefore to the coming out crowds to be baptized by him; Offspring of vipers, who forewarned you to flee from the soon coming wrath?
Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 do produce therefore fruits worthy of repentance; and not may begin to say in yourselves; [As] father We have Abraham. I say for to you that is able God from stones these to raise up children to Abraham.
Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
9 Already now also the ax to the root of the trees is applied; every therefore tree not producing fruit good is cut down and into [the] fire is thrown.
Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
10 And were asking him the crowds saying; What then (shall we do? *N+kO)
Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
11 Answering now (he was saying *N+kO) to them; The [one] having two tunics he should impart to the [one] none having and the [one] having food likewise he should do.
Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
12 Came then also tax collectors to be baptized and they said to him; Teacher, what (shall we do? *N+kO)
Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
13 And he said to them; Nothing more beyond that appointed to you do collect.
Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
14 Were asking then him also those being soldiers saying; What (may do *N+kO) also we ourselves And he said (to *k) (to them; *N+kO) No one may extort nor may accuse falsely and do be content with the wages of you.
Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
15 When were expecting then the people and wondering all in the hearts of them concerning John, whether whether he himself would be the Christ,
Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
16 Answered saying ([to] all *N+kO) John: I myself indeed with water baptize you; comes however the [One] mightier than I, of whom not I am worthy to untie the strap of the sandals of Him. He himself you will baptize with [the] Spirit Holy and with fire,
Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
17 of whom the winnowing fork [is] in the hand of Him (and *k) (to scour *N+kO) the threshing floor of Him and (to gather *N+kO) the wheat into the barn of Him. But the chaff He will burn up with fire unquenchable.
Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
18 Many indeed therefore other things exhorting he was evangelising the people.
Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
19 And Herod the tetrarch being reproved by him concerning Herodias the wife (of Philip *K) of the brother of him and concerning all that did [the] evils Herod,
Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
20 added yet this to all: Also he locked up John in prison.
Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
21 It came to pass now in baptizing all the people and when Jesus having been baptized and having prayed [was] opening the heaven
Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
22 and descending the Spirit Holy in a bodily form (as *N+kO) a dove upon Him and a voice out of heaven coming (saying: *k) You yourself are the Son of Mine the beloved, in You I am well pleased.
kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
23 And Himself was Jesus beginning about years [old] thirty being son, as was supposed of Joseph of Heli
Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
24 of Matthat of Levi of Melchi of Jannai of Joseph
dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
25 of Mattathias of Amos of Nahum of Esli of Naggai
dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
26 of Maath of Mattathias of Semein (of Josech *N+kO) (of Joda *N+kO)
dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
27 of Joannen of Rhesa of Zerubbabel of Shealtiel of Neri
dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
28 of Melchi of Addi of Cosam of Elmadam of Er
dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
29 (of Joshua *N+kO) of Eliezer of Jorim of Matthat of Levi
dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
30 of Simeon of Judah of Joseph of Jonam of Eliakim
dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
31 of Melea of Menna of Mattatha of Nathan of David
dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
32 of Jesse of Obed of Boaz (of Sala *N+kO) of Nahshon
dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
33 of Amminadab (of Admin *N+KO) (of Arni *NO) of Hezron of Perez of Judah
dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
34 of Jacob of Isaac of Abraham of Terah of Nahor
dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
35 of Serug of Reu of Peleg of Heber of Shelah
dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
36 of Cainan of Arphaxad of Shem of Noah of Lamech
dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
37 of Methuselah of Enoch of Jared of Mahalalel of Cainan
dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
38 of Enosh of Seth of Adam of God.
dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.

< Luke 3 >