< Ruth 4 >

1 Now, Boaz, went up to the gate, and sat him down there, and lo! the kinsman, passing by, of whom Boaz had spoken, so he said—Turn aside! and sit down here, such a one! And he turned aside, and sat down.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Then fetched he ten men of the elders of the city, and said—Sit ye down here. And they sat down.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Then said he to the kinsman, The parcel of land that was our brother Elimelech’s, is to be disposed of by Naomi, who hath returned out of the country of Moab;
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 and, I, thought, I would unveil thine ear, saying—Take it over in presence of such as are here seated, and in presence of the elders of my people. If thou wilt act as kinsman, act as kinsman, but, if thou wilt not so act, only tell me—that I may know, for there is none who can set thee aside as kinsman, but, I, am after thee. And he said, I, will act as kinsman.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Then said Boaz, What day thou takest over the land from the hand of Naomi, also, of Ruth the Moabitess, wife of the dead, dost thou take [it], to raise up the name of the dead upon his inheritance.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Then said the kinsman—I cannot act as kinsman for myself, lest I mar my own inheritance, —do, thou, for thyself act as kinsman in my right, for I cannot so redeem.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 Now, this aforetime, [was the way] in Israel, at a redeeming, and at an exchanging, to confirm every word: A man drew off his shoe, and gave it to his neighbour, —yea, this, was the way of taking to witness, in Israel.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 So the kinsman said unto Boaz, Take it over for thyself, —and he drew off his shoe.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 Then said Boaz to the elders, and all the people—Witnesses, are ye to-day, that I have taken over all that was Elimelech’s, and all that was Chilion’s, and Mahlon’s, —from the hand of Naomi:
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 Moreover, Ruth the Moabitess, wife of Mahlon, have I taken over, to be my wife, to raise up the name of the dead upon his inheritance, that the name of the dead be not cut off—from among his brethren, and from the gate of his dwelling- place, —Witnesses, are ye to-day!
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 Then said all the people who were in the gate, and the elders—Witnesses!, —Yahweh grant the woman who is coming into thy house, to be as Rachel, and as Leah, which two of them did build the house of Israel. Do thou bravely, then, in Ephrathah, and proclaim thou a name in Bethlehem,
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 And let thy house be like the house of Perez, whom Tamar bare to Judah, —of the seed which—may Yahweh give thee, of this young woman.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 So Boaz took Ruth, and she became his wife, and he went in unto her, —and Yahweh granted her conception, and she bare a son.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 Then said the women unto Naomi, Blessed, be Yahweh! who hath not let thee fail of a kinsman to-day, —and may his name, be proclaimed, in Israel;
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 So shall he become a restorer of thy life, and a nourisher of thine old age, —for, thy daughter-in-law who loveth thee, hath borne him, even, she, who is better to thee than seven sons.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 So Naomi took the boy, and laid him in her bosom, and she became his nurse.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 And the women, her neighbours, gave him a name, saying, There is born a son to Naomi, —So they called his name Obed, he, was, the father of Jesse, the father of David.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 These, then, are the generations of Perez: Perez, begat, Hezron;
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 And, Hezron, begat, Ram, and, Ram, begat, Amminadab;
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 And, Amminadab, begat Nahshon, and, Nahshon, begat, Salmon,
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 And, Salmon, begat, Boaz, and, Boaz, begat, Obed;
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 And, Obed, begat, Jesse, and, Jesse, begat, David.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Ruth 4 >