< Ruth 3 >

1 Then Naomi her mother-in-law said to her, —My daughter! shall I not seek for thee a place of rest, in which it may be well with thee?
Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
2 Now, therefore, is not, Boaz, of our kindred, with whose maidens thou hast been? Lo! he is winnowing the barley threshing-floor, to-night!
Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
3 Thou wilt, therefore, bathe thee, and anoint thee, and put thine apparel upon thee, and go down to the threshing-floor, —do not make thyself known to the man, until he have done eating and drinking.
Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
4 And it shall be, when he lieth down, that thou shalt mark the place where he doth lie, and shalt go in and turn aside the covering of his feet, and lay thee down, —and, he, will tell thee what thou shalt do.
Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
5 And she said unto her, —All that thou sayest, will I do.
Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
6 So she went down to the threshing-floor, —and did according to all that her mother-in-law had commanded her.
Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
7 And, when Boaz had eaten, and drunk, and his heart was glad, he went in to lie down at the end of the heap of corn. Then came she in softly, and turned aside the covering of his feet, and laid her down.
Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
8 And it came to pass, in the middle of the night, that the man started up, and turned, —and lo! a woman, lying at his feet.
Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
9 And he said, Who art, thou? And she said, I, am Ruth, thy handmaid, spread, therefore, thy wing over thy handmaid, for, a kinsman, thou art.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
10 And he said—Blessed, be thou of Yahweh, my daughter, for thou hast made thy last lovingkindness better than the first, —in not following after young men, whether poor, or rich.
Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
11 Now, therefore, my daughter, do not fear, whatsoever thou shalt say, I will do for thee, —for all the gate of my people doth know, that, a virtuous woman, thou art.
Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
12 And, now, although it is true that, a kinsman, am I, yet is there a kinsman nearer than I.
Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
13 Tarry the night, and it shall be, in the morning, if he will act as kinsman to thee, well, let him so act, but, if he inclineth not to act as kinsman to thee, then will, I, so act to thee—by the life of Yahweh, —Lie still, until the morning.
Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
14 So she lay at his feet, until the morning, and rose up before one could know his neighbour. And he said—Do not let it be known that a woman came into the threshing-floor.
Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
15 And he said—Bring the cloak that is upon thee, and hold it. So she held it, —and he measured six measures of barley, and laid it upon her, and he went into the city.
Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
16 And, when she came unto her mother-in- law, she said—Who art, thou, my daughter? And she told her all that the man had done for her.
Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
17 And she said—These six measures of barley, gave he unto me, —for he said, Do not go in empty, unto thy mother-in- law.
ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
18 And she said—Abide, my daughter, until that thou get to know, how the matter will fall out, —for the man will not rest, except he have finished the thing to-day.
Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”

< Ruth 3 >