< John 3 >

1 There was however, a man from among the Pharisees, Nicodemus, his name, —ruler of the Jews.
akwai wani Bafarise da ake kira Nikodimu, shugaba a cikin Yahudawa.
2 The same, came unto him, by night, and said unto him—Rabbi! we know that, from God, thou hast come, a teacher; for, no one, can be doing, these signs, which, thou, art doing, except, God, be with him.
Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dare ya ce masa, “Rabbi, mun sani cewa kai malami ne da kazo daga wurin Allah, gama ba wanda zai iya yin wadannan alamu da kake yi sai idan Allah na tare da shi.”
3 Jesus answered, and said unto him—Verily, verily, I say unto thee: Except one be born from above, he cannot see the kingdom of God.
Yesu ya amsa masa, “Hakika, hakika, idan ba a sake haifuwar mutum ba, ba zai iya ganin mulkin Allah ba.”
4 Nicodemus saith unto him—How, can a man be born, when he is, old? Can he, into the womb of his mother, a second time, enter, and be born?
Nikodimu ya ce masa, “Yaya za a sake haifuwar mutum bayan ya tsufa? Ba zai iya sake shiga cikin cikin uwarsa kuma a haife shi ba, zai iya?”
5 Jesus answered—Verily, verily, I say unto thee: Except one be born of water and spirit, he cannot enter into the kingdom of God.
Yesu ya amsa, “Hakika, hakika, idan ba a haifi mutum da ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga cikin mulkin Allah ba.
6 That which hath been born of the flesh, is, flesh, and, that which hath been born of the spirit, is, spirit.
Abin da aka haifa ta wurin jiki, jiki ne, kuma abin da aka haifa ta wurin Ruhu, Ruhu ne.
7 Do not marvel, that I said unto thee: Ye must needs be born from above.
Kada ka yi mamaki don na ce maka, 'dole a maya haifuwar ka.'
8 The spirit, where it pleaseth, doth breathe, and, the sound thereof, thou hearest; but knowest not, whence it cometh and whither it goeth: Thus, is every one who hath been born of the spirit.
Iska takan hura duk inda ta ga dama. Ka kan ji motsin ta, amma ba ka san inda ta fito ko inda za ta tafi ba. Haka duk wanda aka haifa daga Ruhu.”
9 Nicodemus answered, and said unto him—How, can these things, come about?
Nikodimu ya amsa yace masa, “Yaya wannan zai yiwu?”
10 Jesus answered, and said unto him—Art, thou, the teacher of Israel, and, these things, knowest not?
Yesu ya amsa yace masa, “Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba?
11 Verily, verily, I say unto thee: What we know, we speak, and, of what we have seen, we bear witness, and, our witness, ye receive not.
Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.
12 If, the earthly things, I told you, and ye believe not, How, if I should tell you the heavenly things, will ye believe?
Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama?
13 And, no one, hath ascended into heaven, save he that, out of heaven, descended, —The Son of Man.
Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.
14 And, just as, Moses, lifted up the serpent in the desert, so, must, the Son of Man, be lifted up, —
Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum
15 That, whosoever believeth in him, may have life age-abiding. (aiōnios g166)
domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada. (aiōnios g166)
16 For God, so loved, the world, that, his Only Begotten Son, he gave, —that, whosoever believeth on him, might not perish, but have life age-abiding. (aiōnios g166)
Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami. (aiōnios g166)
17 For God, sent not, his Son into the world, that he might judge the world, but, that the world might be saved through him.
Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa.
18 He that believeth on him, is not to be judged: he that believeth not, already, hath been judged, —because he hath not believed on the name of the Only Begotten Son of God.
Duk wanda ya bada gaskiya gare shi ba a kayar da shi ba, amma duk wanda bai bada gaskiya gare shi ba an riga an kayar da shi, domin bai bada gaskiya ga sunan wannan da shi kadai ne Dan Allah ba.
19 And, this, is the judgment: That, the light, hath come into the world, —and men loved, rather the darkness than the light, for, wicked, were their, works.
Wannan shi ne dalilin shari'ar, domin haske ya zo duniya, amma mutane suka kaunaci duhu fiye da hasken, sabili da ayyukan su na mugunta ne.
20 For, whosoever doth practise corrupt things, hateth the light, and cometh not unto the light, lest his works should be reproved;
Domin duk wanda ke mugayen ayyuka ya ki haske, kuma baya zuwa wurin hasken domin kada ayyukansa su bayyanu.
21 But, he that doeth the truth, cometh unto the light, that his works may be, made manifest, that, in God, have they been wrought.
Sai dai duk wanda yake aikata gaskiya kan zo wurin hasken domin ayyukansa, da ake aiwatarwa ga Allah, su bayyanu.
22 After these things, came Jesus, and his disciples, into the Judaean land; and, there, was he tarrying with them, and immersing.
Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma.
23 And John also was immersing in Aenon, near to him, because, many waters, were there; and they were coming, and being immersed; —
Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma,
24 for, not yet, had John been cast into prison.
domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.
25 There arose, therefore, a questioning, from among the disciples of John, with a Jew, —concerning purification.
Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa.
26 And they came unto John, and said unto him—Rabbi! he who was with thee beyond the Jordan, unto whom, thou, hast borne witness, see! the same, is immersing; and, all, are coming unto him.
Suka je wurin Yahaya suka ce, “Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa.”
27 John answered, and said—A man can receive, nothing, except it have been given him out of heaven.
Yahaya ya amsa, “Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama.
28 Ye yourselves, unto me, bear witness, that, I, said—I, am not the Christ; but—I am sent before, That One.
Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'
29 He that hath the bride, is, bridegroom; but, the friend of the bridegroom, who standeth by and hearkeneth unto him, greatly, rejoiceth, by reason of the voice of the bridegroom. This, my joy, therefore, is fulfilled.
Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan.
30 That One, it behoveth to increase, —but, me, to decrease.
Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.
31 He that, from above, doth come, over all, is: he that is of the earth, of the earth, is, and, of the earth, doth speak: he that, out of heaven, doth come, over all, is,
Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa.
32 What he hath seen and heard, of, the same, he beareth witness, —and, his witness, no one, receiveth: —
Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa.
33 He that hath received his witness, hath set seal—that, God, is, true.
Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.
34 For, he whom God hath sent, the sayings of God, doth speak; for, not by measure, giveth he the Spirit.
Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba.
35 The Father, loveth the Son, and, all things, hath given into his hand.
Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa.
36 He that believeth on the Son, hath life age-abiding: whereas, he that yieldeth not unto the Son, shall not see life, —but, the anger of God, awaiteth him. (aiōnios g166)
Shi wanda ya bada gaskiya ga Dan ya na da rai madawwami, amma wanda ya ki yiwa Dan biyayya ba zai ga rai ba, amma fushin Allah na kansa. (aiōnios g166)

< John 3 >